An gano shanu 25 da suka ɓace a dajin Sakkwato
Published: 3rd, May 2025 GMT
Hedikwatar ’yan sandan Gada da ke Jihar Sakkwato ta gano wasu shanu 25 da ake zargin an sace ko kuma sun ɓace daga hannun masu su.
An gano dabbobin ne a wani dajin da ke kan iyaka da ƙaramar hukumar Sabon Birni ta jihar a ranar Alhamis, bayan da hukumomin yankin suka samu labarin.
’Yan kungiyar asiri: Mutum 95 sun shiga hannu a Edo Shettima zai halarci bikin rantsar da sabon shugaban ƙasar GabonJami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, Ahmad Rufa’i ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a, inda ya ce an gano dabbobin ne bayan da Alhaji Muhammad Kyari ya bayar da rahoton cewa akwai shanun da suka ɓace.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Hakimin Gada, Alhaji Idi ‘M, tsohon Hakimin garin Gidan Rabami da ke ƙaramar Hukumar Gada, a baya ya sanar da hukuma game da wasu baƙin shanu a wani dajin da ke kusa.
“An gano dabbobin ne a wani dajin da ke da iyaka da ƙaramar hukumar Sabon Birni, yankin da ya shahara da sarƙaƙiya da kuma ƙalubalen tsaro a wasu lokuta.
“Rundunar ’yan sanda ta Gada ta mayar da martani cikin gaggawa, inda ta tura jami’anta zuwa wurin da aka yi nasarar ƙwato shanu 25 ba tare da wata matsala ba.”
Sanarwar ta ci gaba da cewa, bayan kuɓutar da su an kai shanun zuwa hedikwatar Gada, inda ake tsare da su cikin ƙoshin lafiya.
Rundunar ’yan sandan ta yi kira ga masu dabbobin da suka rasa shanunsu da su ziyarci hedikwatar tare da ingantacciyar hujjar mallakar su domin tantancewa tare karɓarsu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Barayin Shanu jihar Sokoto
এছাড়াও পড়ুন:
Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
Gwamnatin Tarayya ta ce Najeriya na rasa sama da Dala Biliyan 10 duk shekara sakamakon asarar amfanin gona bayan girbi.
Ministan Noma Sanata Abubakar Kyari ne ya bayyana haka a wajen kaddamar da shirin Hanyar Inganta Noma da Kayayyakin Mire Rayuwa a Yankunan Karkara G.R.A.I.N a ƙaramar hukumar Birnin Kudu ta Jihar Jigawa.
Ya ce asarar na faruwa ne saboda rashin ingantattun wuraren ajiya, karancin ababen more rayuwa, sauyin yanayi da kuma ambaliya.
Kyari ya bayyana cewa noma na bada gudunmawar kashi 24 bisa 100 na Jimillar Darajar Kayayyaki da Ayyuka da Kasa ta Samar a Cikin Shekara GDP, inda ƙananan manoma ke samar da sama da kashi 70 bisa 100 na abincin da ake ci a ƙasa.
Ya jaddada cewa gwamnati za ta tallafa musu da kayan noma na zamani da wuraran kasuwanci domin inganta tattalin arziki.
A nasa jawabin, Gwamna Umar Namadi na Jigawa ya yaba da samun Cibiyar Cigaban Karakara ta Pulse ta farko a Jigawa, yana mai cewa za ta kawo sauyi a harkar noma da rayuwar jama’ar karkara.
Haka zalika, shi ma Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, ya ce haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu zai taimaka wajen ci gaban tattalin arziki.
Shugaban ƙaramar hukumar Birnin Kudu, Alhaji Builder Muhammad Uba, ya jaddada goyon bayansa ga shirin Renewed Hope Agenda na Shugaba Tinubu tare da yabawa gwamnatin Namadi kan sauya fasalin noma a jihar.
Usman Muhammad Zaria