An gano shanu 25 da suka ɓace a dajin Sakkwato
Published: 3rd, May 2025 GMT
Hedikwatar ’yan sandan Gada da ke Jihar Sakkwato ta gano wasu shanu 25 da ake zargin an sace ko kuma sun ɓace daga hannun masu su.
An gano dabbobin ne a wani dajin da ke kan iyaka da ƙaramar hukumar Sabon Birni ta jihar a ranar Alhamis, bayan da hukumomin yankin suka samu labarin.
’Yan kungiyar asiri: Mutum 95 sun shiga hannu a Edo Shettima zai halarci bikin rantsar da sabon shugaban ƙasar GabonJami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, Ahmad Rufa’i ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a, inda ya ce an gano dabbobin ne bayan da Alhaji Muhammad Kyari ya bayar da rahoton cewa akwai shanun da suka ɓace.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Hakimin Gada, Alhaji Idi ‘M, tsohon Hakimin garin Gidan Rabami da ke ƙaramar Hukumar Gada, a baya ya sanar da hukuma game da wasu baƙin shanu a wani dajin da ke kusa.
“An gano dabbobin ne a wani dajin da ke da iyaka da ƙaramar hukumar Sabon Birni, yankin da ya shahara da sarƙaƙiya da kuma ƙalubalen tsaro a wasu lokuta.
“Rundunar ’yan sanda ta Gada ta mayar da martani cikin gaggawa, inda ta tura jami’anta zuwa wurin da aka yi nasarar ƙwato shanu 25 ba tare da wata matsala ba.”
Sanarwar ta ci gaba da cewa, bayan kuɓutar da su an kai shanun zuwa hedikwatar Gada, inda ake tsare da su cikin ƙoshin lafiya.
Rundunar ’yan sandan ta yi kira ga masu dabbobin da suka rasa shanunsu da su ziyarci hedikwatar tare da ingantacciyar hujjar mallakar su domin tantancewa tare karɓarsu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Barayin Shanu jihar Sokoto
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta yi Allah-wadai da sabon takunkumin da Amurka ta lafta mata
Iran ta yi tir da Allah-wadai da sabbin takunkuman da Amurka ta lafta mata.
Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta bakin kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta ce matakin wata babbar alama ce da ke nuna cewa Washington ba ta da kyakyawar niyya, hasali ba abar yarda ce ba.
Sanarwar ta bayyana karara cewa Iran ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen matsin lamba na Amurka kuma ta dage kan yin shawarwari a karkashin sharudda guda.
Iran na cewa takunkuman da Amurka ke bayyanawa da matsin lamba mafi girma, tun zuwa gwamnatin Trump, ba zasu tankwaso Tehran ba game da hakokkinta.
Kalaman na zuwa ne jim kadan bayan da sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio ya sanar da kakaba wasu sabbin takunkumi kan hukumomi bakwai da jiragen ruwa guda biyu bisa zargin suna da hannu a cinikin man fetur na Iran.
Matakin na zuwa ne jim kadan bayan Iran ta sanar da cewa za a sake gudanar da zagaye na hudu na tattaunawa da Amurka a birnin Rome a ranar Asabar 3 ga watan Mayu a karkashin jagorancin kasar Oman.