Gaza : Kungiyar Euro-Med ta bukaci a binciki harin Isra’ila kan jirgin ruwan Freedom Flotilla
Published: 3rd, May 2025 GMT
Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Euro-Mediterranean (Euro-Med) ta yi kira da a gudanar da bincike mai zaman kansa kan harin da jiragen yakin Isra’ila suka kai kan wani jirgin ruwan Freedom Flotilla da ke dauke da kayan agaji zuwa zirin Gaza da aka yi wa kawanya.
An kai harin ne a ruwan kasa da kasa kusa da Malta.
A cikin wata sanarwa da ta fitar, Euro-Med ta yi kira da a gudanar da bincike mai zaman kansa da gaskiya a karkashin ikon Malta, tare da halartar Majalisar Dinkin Duniya.
Kungiyar mai hedkwata a birnin Geneva ta jaddada cewa dole ne a hukunta wadanda suka aikata irin wannan ta’asa.
Kungiyar ta kara da cewa “Hare-haren da aka kai kan jirgin ruwan farar hula da gangan a cikin ruwa na kasa da kasa, ya zama cin zarafi ga Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya, da dokar teku da kuma yarjejeniyar Roma, wadda ta haramta kai hare-hare kan abubuwan jin kai,” in ji kungiyar, inda ta kara da cewa rashin daukar mataki zai kara karfafa kai hare-hare kan ayyukan jin kai da kuma kara ta’azzara bala’in da ke kunno kai a Gaza.
Wannan harin dai wani bangare ne na yin amfani da karfi da aka saba yi, domin hana jiragen ruwan jin kai isa zirin Gaza, tun ma kafin su tunkari gabar tekun.
A halin da ake ciki kungiyoyin gwagwarmayar Palasdinawa na Hamas da Islamic Jihad sun yi Allah wadai da harin da Isra’ila ta kai kan jirgin ruwan na ‘Freedom Flotilla’, suna masu bayyana hakan a matsayin na ‘yan fashin teku da kuma “keta dokokin kasa da kasa.”
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: jirgin ruwan
এছাড়াও পড়ুন:
Xi Ya Bukaci Matasa Da Su Ba Da Gudummawar Cimma Nasarar Zamanantar Da Kasa
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya bukaci matasan kasarsa da su zage damtse, wajen bayar da gudummawar cimma nasarar zamanantar da kasa, ta hanyar yin dukkanin sadaukarwa da kasar ke bukata daga gare su.
Shugaba Xi, ya yi wannan tsokaci ne cikin martanin wasikar da ya aike ga rukunin malamai masu aikin sa kai, a wata makaranta dake yankin kan iyakan kasar mai nisa, karkashin jihar Xinjiang ta Uygur mai cin gashin kai dake arewa maso yammacin kasar Sin. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp