Gaza : Kungiyar Euro-Med ta bukaci a binciki harin Isra’ila kan jirgin ruwan Freedom Flotilla
Published: 3rd, May 2025 GMT
Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Euro-Mediterranean (Euro-Med) ta yi kira da a gudanar da bincike mai zaman kansa kan harin da jiragen yakin Isra’ila suka kai kan wani jirgin ruwan Freedom Flotilla da ke dauke da kayan agaji zuwa zirin Gaza da aka yi wa kawanya.
An kai harin ne a ruwan kasa da kasa kusa da Malta.
A cikin wata sanarwa da ta fitar, Euro-Med ta yi kira da a gudanar da bincike mai zaman kansa da gaskiya a karkashin ikon Malta, tare da halartar Majalisar Dinkin Duniya.
Kungiyar mai hedkwata a birnin Geneva ta jaddada cewa dole ne a hukunta wadanda suka aikata irin wannan ta’asa.
Kungiyar ta kara da cewa “Hare-haren da aka kai kan jirgin ruwan farar hula da gangan a cikin ruwa na kasa da kasa, ya zama cin zarafi ga Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya, da dokar teku da kuma yarjejeniyar Roma, wadda ta haramta kai hare-hare kan abubuwan jin kai,” in ji kungiyar, inda ta kara da cewa rashin daukar mataki zai kara karfafa kai hare-hare kan ayyukan jin kai da kuma kara ta’azzara bala’in da ke kunno kai a Gaza.
Wannan harin dai wani bangare ne na yin amfani da karfi da aka saba yi, domin hana jiragen ruwan jin kai isa zirin Gaza, tun ma kafin su tunkari gabar tekun.
A halin da ake ciki kungiyoyin gwagwarmayar Palasdinawa na Hamas da Islamic Jihad sun yi Allah wadai da harin da Isra’ila ta kai kan jirgin ruwan na ‘Freedom Flotilla’, suna masu bayyana hakan a matsayin na ‘yan fashin teku da kuma “keta dokokin kasa da kasa.”
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: jirgin ruwan
এছাড়াও পড়ুন:
Yarima Mai Jiran Gadon Saudiyya Ya Jaddada Goyon Bayan Kasarsa Ga Iran
Yarima mai jiran gadon Saudiyya ya tabbatarwa shugaban kasar Iran cewa: Saudiyya tana goyon bayan Iran
Yariman mai jiran gadon Saudiyya Mohammed bin Salman ya tabbatar da hakan ne a wata tattaunawa ta wayar tarho da shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian a yammacin jiya Asabar, yana mai jaddada cewa: Masarautar Saudiyya da daukacin al’ummar musulmin duniya sun hadu a kan goyon bayan Iran.
Yarima mai jiran gadon sarautar Saudiyya ya ce: Dukkanin al’ummomin kasashen musulmi a yau suna da hadin kai da jaddada goyon bayansu ga Iran, kuma yana iyaka kokarinsa a fagen diflomasiyya da matsin lamba na kasa da kasa don dakatar da wuce gona da irin da ‘yan sahayoniyya suke yi kan Iran.
Bin Salman ya yi Allah wadai da hare-haren rashin adalci da ‘yan sahayoniyya suke kaiwa Iran.
Ya kuma bayyana jimaminsa tare da jajantawa al’ummar kasar Iran dangane da wadannan hare-hare da suka rutsa da su, yana mai jaddada cewa: Saudiyya tana da tabbataccen matsayi kan tsayawa tare da ‘yar uwarta Jamhuriyar Musulunci ta Iran, kuma duniyar musulmi a yau ta hade kan muryar daya wajen goyon bayan Iran.
Ya ci gaba da cewa: “Mun yi imanin cewa, gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila na neman ta hanyar kara kunna wutar rikici ta janyo Amurka a cikin tsakiyar rikici, amma suna da yakinin cewa martanin Iran a kan ma’aunin daidaito da matakan hankali zai dakile wannan yunƙurin makirci.”
Bin Salman ya kuma jaddada cewa: Kasarsa ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen bayar da duk wani tallafi da ya dace ga ‘yan uwanta Iran.