Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja
Published: 3rd, May 2025 GMT
Wasu daga cikin manoman a wadanan yankuna sun bayyana cewa, sun koma neman wasu gonakin da za su yi shuka ko dai a cikin jihar ko kuma a wasu guraren daban, musamman duba da cewa; sun dogara ne a kan wadannan sana’o’i na noma da kamun Kifi.
Koda-yake dai, gwamnatin tarayya ta yi wani gini mai tsawon zurfin kimanin mita bakwai da nufin dakile ambaliyar ruwan daga Kogi, amma tuni ginin ya rushe tun daga farkon aikin.
An dai gaza sake yin aikin ginin, yau kusan shekara uku zuwa hudu.
Bugu da kari, tuni wasu gonaki, musamman a yankin na Muye da ake da kadada 2.6, aikin yin noma ya tsaya cak, inda kuma mazauna yankin a halin yanzu ke zuwa wasu guraren, domin hada-hadar saye da sayarwar amfanin gona.
Wani mazaunin yankin, Ebwa Ibrahim Saidu ya sanar da cewa; akwai bukatar samar da daukin gaggawa a kan wannan matsala.
“Wasu manoma a yankin, sun koma wasu yankunan, domin neman gonakin da za su yi noma, domin ba za iya sake yin wani noma a gonakin nasu ba, sakamakon faruwar wannan matsala,” in ji Ibrahim.
Ya ce, akasarin matasanmu yanzu, sun koma Jihar Kogi don yin harkar Achaba.
Shi ma Dagacin Muye, Alhaji Salihu Muhammad ya tabbatar da wannan matsala.
“An yi aikin sake gina madatsar ruwar ne, tun bayan shekara uku zuwa hudu da suka gabata, wacce kuma ta sake rushewa a lokacin kakar noman bara, wanda hakan ya jawo lalata gonakinmu da dama“.
“Gwamnatocin baya, sun yi kokrin sake gina madatsar ruwan, amma idan Kogin ya yi ambaliya, sai ta sake lalacewa“ in ji Salihu.
Kazalika, Mukaddashin Manajan Darakta na Riko a Hukumar Samar da Wutar Lantarki ta Kasa (N-HYPPADEC), Mista Jimoh Haruna Gabi, a lokacin kaddamar da sake aikin ginin madatsar ruwan ya sanar da cewa, aikin zai lakume sama da Naira miliyan 600.
Ya kara da cewa, hukumar ta sake gyara kadadar noma 2.6, domin manona su sake komawa gonakinsu, don fara nomansu.
A cewarsa, sake aikin na madatsar ruwan, ana sa ran kammalawa a watan Yuli, kafin ruwan sama ya fara sauka a watan Agusta.
Shi ma, dan Majalisa mai wakiltar mazabar Agaie/Lapai ta tarayya Abdullahi Mahmud, ya bukaci a samar wa da manoman wadannan yankunan dauki, musamman duba da cewa; sana’ar noma ce akasarin al’ummar wadannan yankuna, suka mayar da hankali a kai.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
’Yan fashin teku sun sace mata 4 a hanyar ruwa na Bayelsa
Wasu ’yan bindiga da ake zargin ’yan fashi ne sun kai hari kan wani jirgin ruwa da ke jigilar mata ’yan kasuwa zuwa Ƙaramar hukumar Ijaw ta Kudancin Jihar Bayelsa, a kan hanyar ruwan Lobia/Foropa.
Rahotanni sun ce maharan sun yi garkuwa da wasu mata huɗu a lokacin da lamarin ya faru a ranar Talata.
NAJERIYA A YAU: Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta Najeriya za ta karɓi baƙuncin Gasar Karatun Alkur’ani ta Duniya a karon farkoWata majiyar unguwar da lamarin ya faru ta shaida wa Daily Trust a safiyar ranar Alhamis, maharan sun kai harin ne ’yan mintuna kaɗan bayan jirgin ruwan fasinjan ya tashi daga gaɓar ruwan Swali a Yenagoa, babban birnin jihar.
Ya ce, kimanin mutane 12 da ke cikin kwale-kwalen an ƙwace dukiyoyinsu da kuɗaɗensu, yayin da ’yan fashin suka yi awon gaba da huɗu daga cikin matan zuwa cikin daji ba tare da sanin dalilansu ba.
A halin yanzu, Ɗan majalisa mai wakiltar mazaɓar Ijaw ta kudu ta 4 a majalisar dokokin Jihar Bayelsa kuma shugaban kwamitin kare haƙƙin ɗan Adam na majalisar Honorabul Selekaye Victor-Ben, ya yi Allah wadai da lamarin.
Ya kuma bayyana sace mutanen a matsayin harin da aka kai wa waɗanda ba su ji ba ba su gani ba.
A cewarsa, “Ba wai cin mutuncin bil’adama ba ne kawai, har ma da babbar barazana ga zaman lafiya da tattalin arzikin mazaɓarmu da ma jihar baki ɗaya.
“Ina yin Allah wadai da wannan ta’addanci da kakkausar murya kuma ina bayar da haɗin kai tare da iyalan waɗanda abin ya shafa a wannan lokaci mai tsanani.”
Ya kuma yi kira ga gwamnatin Jihar Bayelsa da dukkanin hukumomin tsaro da abin ya shafa, musamman rundunar ’yan sandan Najeriya da su gaggauta sakin waɗannan matan da aka sace ba tare da wani sharaɗi ba.