Aminiya:
2025-05-27@20:24:41 GMT

Yadda aka yi bikin yaye sabbin matuƙa jiragen Rundunar Sojin Saman Najeriya

Published: 2nd, May 2025 GMT

Rundunar Sojin Sama ta Najeriya ta yaye sabbin matuƙa jiragen sama 35 bayan sun kammala samun horo.

Babban Hafsan Rundunar, Iya Mashal Hassan Abubakar, ne ya sanya sabbin matuƙa jiragen anini a yayin bikin da aka gudanar a Makarantar Tukin Jirgi na rundunar (401 FTS) da ke Kaduna.

Yayen nasu ya zo ne watanni kaɗan bayan rundunar ta mallaki sabbin jiragen yaki guda 12, waɗanda suka ƙara mata ƙaimi wajen ayyukan samar da tsaro da kuma ta’addanci.

A wani taro da ya gudanar da tsofaffin sojojin rundunar a Kaduna, Iya Marshal Hassan Abubakar ya shaida musu cewa rundunar tana jiran karin jiragen yaƙi guda 34.

Ya buƙaci waɗanda aka yayen nasu da su yi amfani da wannan dama wajen cika burin ’yan Najeriya da ke da kyakkyawan fata a kansu.

Rundunar na da nufin amfani da sabbin matuƙan jiragen nata a ayyukanta na tabbatar da tsaro a sassan kasar nan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jirage Rundunar

এছাড়াও পড়ুন:

Wani abu ya fashe kusa da barikin soji a Abuja

Rundunar ‘yan sandan Birnin Tarayya ta buƙaci al’ummar da ke kewayen hanyar Mararaba zuwa Nyanya su kwantar da hankalinsu bayan jin ƙarar wani abu da ya fashe a yammacin ranar Litinin.

Lamarin ya faru ne a wata tashar bas da ke kusa da barikin sojoji na Mogadishu a kan hanyar Mararaba zuwa Nyanya.

A wata sanarwa da rundunar ta fitar mai ɗauke da sa hannun kakakinta, Josephine Adeh, ta ce tuni ta tura jami’anta wajen domin bincike da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin.

Kwastam ta kama Tiramol ta N150m, ta miƙa wa NAFDAC a Kano FCTA ta rufe hedikwatar PDP saboda rashin biyan haraji

“A ranar 26 ga watan Mayu da misalin ƙarfe 2:15 na rana aka yi mana kiran gaggawa kan wani abu ya fashe a shatale-shatalen hanyar Mararaba-Nyanya.

“Muna samun rahoton jami’anmu da ke sashen da abun ya shafa suka dira a wajen in da suka kange wurin.

“Mun samu nasarar ceto mutum guda da ya samu rauni, kuma yana asibiti yana karɓar magani.

“Muna nan muna bincike domin gano abin da ya fashe, da kuma musabbabin hakan.

Daga nan ne rundunar ta bukaci al’ummar yankin su ci gaba da harkokinsu ba tare da wata fargaba ba, su kuma miƙa wa rundunar duk wani motsi da ba su amince da shi ba.

Rahotanni sun bayyana cewa wanda ya tayar da bam ɗin ya mutu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rundunar Ƴansanda Ta Gayyaci Jami’anta Da Bidiyonu Ya Yaɗu Suna Karɓar Cin Hancin Naira 5000
  • NAJERIYA A YAU: Matsalolin Da Suke Tarnaki Ga Kananan Yara A Najeriya Da Hanyoyin Magance Su
  • Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano
  • Wani abu ya fashe kusa da barikin soji a Abuja
  • ‘Yansanda Sun Nemi A Kwantar Da Hankula Bayan Fashewar Wani Abu A Abuja
  • Iran Ta Kira Yi Jakadan Faransa Akan Furucin Ministan Harkokin Wajen Kasarsa
  • NAJERIYA A YAU: Tasirin Dangantakar Bangaren Zartarwa Da Na Majalisa A Kan Talaka
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 5 A Katsina
  • An kama Hakimi kan zargin taimaka wa ’yan bindiga a Neja
  • Rasha Ta Tarwatsa Makaman Ukiraniya A Tashar Jiragen Ruwa Ta Odessa