Hamas Ta Yi Allah Wadai Da Matsayin Amurka Na Goyon Bayan Haramta Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijiran Falasdinawa Ta UN
Published: 2nd, May 2025 GMT
Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta yi Allah wadai da matsayin Amurka na goyon bayan haramta hukumar kula da ‘yan gudun hijira falasdinawa ta Majalisar Dinkin Duniya (UNRWA)
Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta yi Allah wadai da matsayin Amurka na goyon bayan haramtacciyar kasar Isra’ila kan haramta hukumar kula da ‘yan gudun hijiran Falasdinawa da ayyukan ba da agaji ta Majalisar Dinkin Duniya “UNRWA”, tana daukan wanan a matsayin Amurkia na ci gaba da nuna son kai da goyon bayan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ‘yar mamaya da kuma rashin mutunta dokokin kasa da kasa da yarjejeniyar jin kai.
A cikin wata sanarwar manema labarai da ta fitar jiya Alhamis, kungiyar Hamas ta yi nuni da cewa: Shigar da Amurka ta yi a baya-bayan nan a gaban kotun kasa da kasa domin ganin an yi watsi da zarge-zargen da ake yi kan aikata laifuka yaki kan ‘yan sahayoniyya, ya yi daidai da matsayar gwamnatin mamayar Isra’ila, da ke da nufin gurgunta rawar da hukumar UNRWA ke takawa wajen yi wa ‘yan gudun hijirar Falasdinu hidima, da kuma tsaurara matakan tsaro a zirin Gaza, yayin da ake ci gaba da aiwatar da “laifi na kakaba masifar yunwa” kan fararen hula.
Kungiyar Hamas ta ce zargin da gwamnatin mamayar Isra’ila ke yi wa hukumar UNRWA ta Majalisar Dinkin Duniya “karya ce karara” da nufin kawar da rawar da hukumar ta UNRWA ke takawa da kuma kawo karshen ayyukan jin kai da ta ke yi musamman kan batun ‘yan gudun hijirar Falasdinu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
NEMA Ta Karɓi ‘Yan Nijeriya 203 Da Suka Maƙale A Libya
Haka kuma wasu hukumomin gwamnati sun taimaka, ciki har da Hukumar ‘Yan Gudun Hijira ta Ƙasa, Hukumar Shige da Fice, Hukumar Tsaro ta DSS, Hukumar Lafiya ta Tashar Jirgin Sama da Rundunar ‘Yansanda.
Mutane biyu daga cikin waɗanda aka dawo da su na fama da matsananciyar rashin lafiya, kuma an garzaya da su asibitin New Ikeja don a duba lafiyarsu.
Bayan an yi musu rijista da ɗaukar bayanan yatsunsu, an mayar da su cibiyar mazauna ‘yan gudun hijira da ke Igando, a Jihar Legas, inda za su samu taimako don ci gaba da rayuwa.
NEMA ta ce wannan wani ɓangare ne na ƙoƙarinta na tallafa wa ‘yan Nijeriya da ke cikin mawuyacin hali a ƙasashen waje da kuma taimaka musu su farfaɗo da rayuwarsu cikin aminci a gida.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp