Aminiya:
2025-06-17@03:09:45 GMT

Wulaƙancin da ake mana a Kudu ya yi yawa —Hausawan Legas

Published: 2nd, May 2025 GMT

Al’ummar Arewa mazauna yankin Obalande da ke Jihar Legas sun yunƙura domin tunkarar matsalolin da ke ci musu tuwo a ƙwarya, musamman yadda suka ce ’yan ƙasa ke musu cin kashi.

Sun ce sun gaji da irin tsangwama da ƙasƙanci da ’yan ƙasa a yankin ke nuna wa ’yan Arewa, musamman Hausawa mazauna.

Sun bayar da misali bisa yadda samarin Yarabawa daga wasu unguwanni suka mayar da unguwar tasu filin ƙwallon ƙafa, inda suke tilasta musu rufe rumfunansu na kasuwa, har sai an gama buga ƙwalon kafin su ci gaba da sana’arsu.

A kan haka ne suka yi wani zama da Shugaban Karamar Hukumar Ikoyi Obalande (LCDA) Fu’ad Lawal Atanda da shugabannin siyasa ’yan Arewa a jihar, da nufin cire kitse daga wuta.

NAJERIYA A YAU: Yadda naira biliyan ɗaya ta salwanta a gobarar Kasuwar Jos Sojoji sun ceto fasinjoji 99 daga hatsarin kwale-kwale a Ribas Gwamnonin Arewa maso Gabas sun buƙaci a ɗauki mataki kan matsalolin yankin

Taron ya kuma tattauna kan matsalar lalacewar tarbiyya da shaye-shaye da karuwanci da baɗala da wasu matasan yankin da sauran ɓata-gari ke yaɗawa.

Yadda ake mana cin kashi — Gulma

Jagoran taron kuma Shugaban Majalisar Shugabannin ’Yan Arewa na Ƙananan Hukumomim Jihar Legas, Alhaji Sa’adu Gulma, ya shaida wa Aminiya cewa, dalilin shirya taron shi ne ƙalubalen da ’yan Arewa ke fama da su cikin unguwar Obalende.

Alhaji Sa’adu Gulma, wanda ya ce ya fi shekara 40 a Obalende, ya ce “Yarabawan wasu unguwanni ke shigo mana, su tilasta wa ’yan kasuwarmu rufe rumfunan kasuwanci da sunan buga ƙwallon ƙafa. Ku ma ’yan jarida a yau kuna gani yadda matasan Yarabawan suka rufe mana layi, suna buga ƙwallo, sun tilasta wa ’yan kasuwarmu rufe kantinansu.

“Haka suke yi, wani lokaci sai su zo nan tun safe ba za za su tashi ba sai bayan sallar Azahar, babu Lahadi, babu Litinin duk lokacin da suka ga dama suke shigo mana, ba ka isa ka buɗe kantinka ba, saboda suna ƙwallo.

“Waɗannan abubuwan ne ke ci mana tuwo a ƙwarya da suka sa muka farka, muka kira wannan taro, domin mu sama wa kanmu mafita. Idan muka haɗa kai muka nema wa kanmu mafita, za su kiyaye mu, domin sai bango ya tsage ƙadangare zai shiga, ya sami mafaka.

“Ba za mu yarda amfaninmu ya zama kawai lokacin siyasa ba, ta yadda za a yi amfani da mu idan an ci moriyar ganga a jefar da kaurenta” in ji shi.

‘Ko a mafarki ban tava tunani ba’

Game da lalacewar tarbiyya a yankin, Alhaji Zakari Zaki, ya ce, ko a mafarki bai taɓa tunanin abin da ke faruwa a yankin ba.

Ya shaida wa Aminiya cewa, “Na kasance a wannan unguwar sama da shekara 43, kuma a wancan lokacin abin da ke faruwa a yanzu ko a marfarki ban taɓa zaton za mu sami kanmu cikin wannan hali ba, kuma kowa ya yi shiru.

“Abu na farko babu shugabanci, abin da ya sa na ce babu shugabanci, a baya muna da Shugaba Hamza Kolo, a nan zai fito shan iska za ka ga manyan shugabannin ƙasa irin su Abacha da Babangida da sauransusu, sun zo sun zauna tare da shi, suna hira.

“A wancan lokacin babu shiririta irin su harkar shaye-shaye ko karuwanci a nan, sai dai kyawawan al’adunmu na gargajiyar Arewa, amma a yanzu a wannan unguwar zai yi wuya ka bambamce matar aure da karuwa.

“Sannan abu na biyu mutanenmu da ke shigowa kasuwanci ya kamata su sani kowace jiha da irin tata doka da ƙa’idoji. Mutum ne zai zo ya kasa kayan kasuwancinsa a kan hanya, idan ka yi masa magana sai ya ce ‘ai ba kai ka kawo ni Legas ba’. Ka ga wannan matsala ce ta rashin shugabanci.”

Za mu ƙungiyar aiki da cikawa — Zaki

Ya ce, “bayan taron za mu kafa ƙungiyar haxaka ta tabbatar da tsaro da doka da oda a unguwar ta Obalende, kuma za mu kafa ta bisa doka, za mu tuntubi duk mahukunta da suka da ce” in ji shi.

Wazirin Obalende, Alhaji Sale Muhammed Waziri, wanda yana cikin mahalarta taron ya shaida cewa, tabbas mawuyacin halin da Hausawa da sauran ’yan Arewa ’yan Obalende suka sami kansu shi ne rashin shugabanci ko jagoranci na gari.

Ya ce, “Tun da asalin shugabanninmu na baya suka rasu, an rasa waxanda za su jagoranci al’amarin talakawa a Obalende.

“Idan babu shugabanci kyakkyawa, su ma talakawan ba za su zamo masu biyayya ba. Muna fatan kuma a aiwatar da abubuwan da aka faɗa a wajen wannan taro, domin galibi sai an taru an yi gangami an yi abu sai ka ga daga baya an rushe shi, ba a aiwatar da komi ba.

“Muddin za a aiwatar da abubuwan da aka cim ma muna fatan wannan unguwa ta Obalende za ta sami ci gaba, kuma sauran unguwannin Hausawa a Legas za su yi koyi da Obalende”, in ji shi.

‘Abin da ya jawo mana ƙasƙanci a Legas’

Alhaji Sa’adu Gulma ya ce rashin tsari ne ke janyo wa ’yan Arewa mazauna Legas ƙalubalen da suke fuskanta. Ya ce kaɗan daga cikin rashin tsarin sun haɗar da rashin amfani da tsarin katin shaida.

“Mutum ne zai baro gida Arewa, ya zo ci-rani Legas ba shi da wata takarda ko katin shaida da zai nuna daga inda ya fito ko kalar sana’ar da yake, da zarar ya shiga matsala an kai shi gidan yari shi ke nan, babu yadda za a gano ’yan uwansa.

“Idan an zo kame daman shi ba shi da katin shaida, ba za a gane ko na gari ba ne ko ɓata-gari ne, don ba shi da alamar da za a tantance shi. Wannan kaɗan ne daga cikin ƙalubalen da muke fuskanta.

“Su ragowar ƙabilu kowace irin sana’a suke, komai ƙanƙantarta za su yi ƙungiya, za su sami katin shaida na mambobinsu, amma mu a ɓangarenmu na ’yan Arewa muna zaune ne kara zube, dole sai mun gyara kafin mu ga ci gaba.

“Za mu yi zama na musamman da sauran shugabannin ’yan Arewa na Obalende, domin samar da mafita ga matsalolin da ke addabar su”, in ji shi

Gwmanati za ta ɗauki mataki — Ciyaman

Da yake magana a kan koke-koken, Shugaban Ƙaramar Hukumar ya bayyana cewa tarihi ba zai manta da irin gudummawar da iyaye da kakannin ’yan Arewa mazauna Obalande suka bayar ba, yana mai cewa, ya san lokacin da duk wani babba da suka haɗar da shugabannin ƙasa da ’yan majalisun a jamhuriya ta farko suke zuwa Obalande a yi masu ɗinki.

“Yawancin manyan mutanen nan tailolinsu a nan Obalande suke, nan suke zuwa su huta, bayan sun kammala sha’anin mulkin ƙasa, nan suke cin abinci irin na gargajiyarsu, a nan ake yi masu ɗinkuna irin na gargajiya, kuma wannan yanki ne mai zaman lafiya da ba a taɓa samun rikici ko na ƙabilanci ko kuma wani na daban ba.

“Don haka za mu yi duba ga duk matsalolin da ke ci muku tuwo a ƙwarya, kuma maganar masu yin ƙwallo cikin unguwarku, tuni muka samar da filayen ƙwallo, wanda za su iya zuwa can su yi amfani da su, ba tare da sun shigo nan sun addabe ku ba,” a cewarsa.

Fu’ad Lawal ya ce, taron ba na siyasa ba ne, illa kawai a duba hanyoyin magance matsalolin da ke addabar ’yan Arewan, “amma ba zan mance da irin gudummawar da kuka ba ni ba a siyasance tsawon shekaru takwas da na yi ina jagorancin wannan ƙaramar hukuma,” In ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa Hausawa Yarbawa

এছাড়াও পড়ুন:

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

Iyaye su ne ke ginawa yara dabi’un farko, shi ne ma ya sa a ke so su rika kiyaye irin maganganun da za su rika yi a gaban yaransu, sannan su tsaftace mu’amalolinsu ta yadda yaran ba za su rika kwaikwayon abubuwan da ba su dace ba. hatta da yin dakuwa da nufin zagi, a wurin iyaye yara ke fara koyo. Shi ne ya sa za ka ga wani ya zama gwani a zagi, kwararren gaske. Ba a sama ya samo dabi’ar ba, abin da ya taso ya ga a na yi a gidansu kenan. Wasu kuwa gidansu mutanen kirki ne, don haka ba su iya samun daman kwaikwayon zagi a gida.

Daga gida, lokacin da yaro ya fara wayo, ma’ana zai yiwu a kyale shi ya rika fita waje, sannan ya kai shekarun fara zuwa makaranta. Wasu unguwarsu ‘G.R.A’ ne, babu hayaniya; ba irin unguwannin nan ba ne da a ke cakude da juna. A nan, dabi’un yaransu sun fi samuwa a mu’amalar da yaran ke kwaikwayo daga iyaye.

A irin unguwannin da a ke cakude, ma’ana wadanda yawanci ma gidajen haya ne masu mutane rututu, ya na wahala a iya saita dabi’un yaro. Na farko yaro zai rika kwaikwayon dabi’un iyayenshi, sannan zai rika kwaikwayon na ‘yan hayan gidansu, sannan zai rika kwaikwayon na sauran yaran kan layi; da ya ke irin wannan unguwannin kofofi a bude su ke, yaro ko da rarrafe ya ke yi, zai iya fita kan layi. Wasu yaran ma, dabi’un da su ke kwaikwayo wa a kan layi, ya fi karfin sanin iyayensu. A irin wadannan unguwannin mutane sun fi saurin diban dabi’u, masu kyau da marasa kyau.

Idan yaran wadanchan unguwannin ‘G.R.A’, suka fara zuwa makaranta, za su iya haduwa da yaran unguwannin da a ke cakude da juna. A makaranta za su fara musayar dabi’u a tsakanin juna. Mutum ya na kwance a gida, ya yi tsammanin dabi’unshi da na matarshi da mutanen cikin gida kadai dansu ke kwaikwaya, bai san cewa ya na kwaikwayo wasu daga mu’amalarshi da wasu yara a makaranta ba. wannan na faruwa hatta a makarantun Islamiyyoyi.

Ba kawai a yarinta a ke gina dabi’u ko kwaikwayonsu ba, kowanne mataki na rayuwa a na sake kwaikwayon dabi’u ne da gina sabbi. Wani zai taso har ya balaga da dabi’u masu ban sha’awa da burgewa, amma da zaran ya fara makarantar Sakandare ko gaba da Sakandare, sai yanayin mu’amalarsa ta chanza, saboda haduwa da zai yi da wasu sabbin mutane wadanda suka fito daga wurare mabambanta. Idan ba a yi sa’a ya hadu da abokan arziki ba, sai ya hadu da wadanda a hankali za su gina mishi dabi’un shaye-shaye, ko kuma neman mata.

Musamman a jami’o’i, wata yarinyar za ta zo daga gidansu da dabi’un kwarai, babu ruwanta da sa suturar banza. Yawancin irin wadannan ‘yan matan, a kan hada su zama dakin ‘Hostel’ daya da su. Tun kafin ta fara halartan azuzuwa don daukan darasi, tun kafin ta san sauran mutanen ajinsu, da wadannan abokan zaman nata za ta fara mu’amala. Idan ba a dace ba, a hankali za su koya mata dabi’ar fita babu lullubi ballantana hijabi. Idan samarinsu sun zo zance, sai su rika takura mata a kan ta yi musu rakiya, har watarana abokin saurayin ya ganta ya ce ya na so, shi kenan ita ma ta shiga shirgin.

Kowacce irin dabi’ar mutum, idan a na son a rusa ta, ba a garaje, ba a gaggawa, ba kuma a nuna kosawa. A hankali za a rika nunawa wannan dabi’ar rashin dacewarta, da kuma nakasunta. Ba a rusa dabi’a da karfi ko da fada, ba a rusa ta da iko ko nuna isa. Dabi’u sun fi bukatar lalama da sassauci.

Kafin ka iya rusa dabi’ar mutum, dole sai ka yi nazarin yadda ya ke kallon wannan dabi’a ta sa, ma’ana fahimtarsa dangane da dabi’ar. Idan Yaro ne wanda ke shaye – shaye, dole ne sai ka fahimci menene fahimtarsa dangane da shaye-shaye, tare da nazarin abubuwan da suka jefa shi zuwa ga shaye – shayen. Shin akwai wani abu da ya ke kauna? Idan akwai menene wannan abin? Shin ya na samun daman yin tunani, wanda ba a maye ba, a hankalinshi? Idan ya kan samu lokacin yin tunani ba tare da ya sha komi ba, sai ka fahimci wannan lokacin, a sannan ne za a iya fara aikin chanza mishi tunani.

Kafin mutum ya fara wannan dabi’a da a ke son rusawa, dole a baya ya na da wasu dabi’u, kuma ya na da wasu abokai wadanda a bayan ya ke mu’amala da su. Dole a na bukatar sannan wannan. Saboda idan dabi’ar ta yi kamari, dole ne sai an sake dawo mishi da rayuwar da ya yi a baya, an dawo mishi da tsofaffin abokai, sannan a shimfida musu tsarin yadda za su tafiyar da mu’amala a tsakaninsu, idan a ka bi matakan yadda suka dace a kan yi nasarar rusa dabi’ar da ba a so. Sai dai hanzari ba gudu ba, kwaikwayon dabi’a ya fi sauri a kan rusa ta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dan shekara 10 ya harbe mahaifinsa ɗan sanda a Anambra
  • Dan shekara 10 ya kashe mahaifinsa ɗan sanda da bindiga
  • KADSEMA da IOM sun fara tantance ɓarnar da ambaliya ta yi a Kaduna
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Sojojin Isra’ila Sun Kashe Kananan Yara Masu Yawa A Iran
  • Sabon harin Iran ya hallaka mana mutum 8 – Isra’ila
  • An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna
  • Cece-Kuce Ya Barke Bayan Ganduje Da Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas Sun Nemi A Sauya Shettima A 2027
  • NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa
  • Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 
  • Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila