Aminiya:
2025-07-31@17:44:04 GMT

Sakataren PDP: Damagum ya amince da matsayar gwamnoni

Published: 24th, April 2025 GMT

Muƙaddashin Shugaban Jam’iyyar PDP na Ƙasa, Ambasada Umar Damagum, ya umarci jami’an jam’iyyar da su yi karɓi Arch. Setonji Koshoedo a matsayin mukaddashin sakataren jam’iyya na ƙasa.

Gwamnonin PDP, a taron da suka yi a Ibadan, Jihar Oyo, sun amince da Koshoedo a matsayin mukaddashin sakatare har sai lokacin da shugabannin shiyyar Kudu maso Gabas za su zaɓi cikakken sakatare wanda Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) na jam’iyyar zai amince da shi.

Kotun Ƙoli, a hukuncin da ta yanke kan wanda ya cancanci ya riƙe muƙamin tsakanin Sanata Samuel Anyanwu da Sunday Ude-Okoye, ta ba jam’iyyar ikon yanke shawara kan shugabanninta.

Sai dai a wata takarda da Alhaji Gurama Bawa, jami’in gudanarwa na mukaddashin shugaban jam’iyyar ya fitar, ta ce Setonji Koshoedo, Mataimakin Sakatare na Ƙasa (DNS), yanzu shi ne Mukaddashin Sakatare na Ƙasa na babbar Jam’iyyarmu har sai an sanar da wani abu.

Na ba ku wata 1 ku murƙushe ’yan ta’adda — Olukoyede ga sojoji NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Amfani Da Kafofin Sada Zumunta Wajen Haɓaka Kasuwanci

Takardar ta kuma roƙi ma’aikatan jam’iyyar da su ba sabon mukaddashin sakataren goyon baya wajen gudanar da ayyukansa.

Takardar ta ce: “Dangane da abin da ke sama, duk wasiƙun jam’iyyar ya kamata a tura su ga Hon. (Arch) Setonji Koshoedo.

“An roƙe ku da ku ba shi duk goyon baya da haɗin kai da ys dace a matsayinsa na Mukaddashin Sakatare na Ƙasa na babbar Jam’iyyarmu.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: sakataren jam iya

এছাড়াও পড়ুন:

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Melaye wanda shi ne dan takarar gwamna a jam’iyyar PDP a zaben jihar Kogi a 2023, har yanzu bai bayyana jam’iyyar da zai koma ba a nan gaba. Sai dai rahotanni na nuni da cewa, yana iya sauyawa zuwa jam’iyyar ADC – wata gamayyar jam’iyyar adawa da a baya-bayan nan ta jawo hankalin wasu jiga-jigan masu sauya sheka da suka hada da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Peter Obi zai lashe jihohin Arewa idan ya koma PDP – Jerry Gana
  • Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya
  • 2027: Ba Mu Kafa Haɗakarmu Don Cika Burin Atiku Ba – ADC
  • Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
  • Shugabannin Hukumomin Watsa Labarai Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya ga Tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa Aisha Buhari
  • APC Zamfara Ta Taya Sabon Sarkin Katsinar Gusau Murna
  • Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci