Daga nan sai Geng Shuang ya bayyana matsayar kasar Sin don gane da hakan, yana mai cewa, kasar na matukar jajantawa al’ummun Haitian bisa halin da suka shiga. Yana mai kira ga daukacin al’ummun duniya da su ci gaba da taimakawa kasar wajen karfafa tsare-tsarenta na ikon gina kai, da rungumar tafarkin neman ‘yancin kai, da dogaro da kai, da gaggauta hawa turbar neman ci gaba na kashin kai.

Yayin da hakan ke wakana, Sin za ta ci gaba da taka rawar gani tare da dukkanin sassa masu ruwa da tsaki na kasar ta Haiti. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi

Sojojin Nijeriya a Lokoja, tare da haɗin gwuiwar sauran hukumomin tsaro, sun kuɓutar da mutane shida da aka yi garkuwa da su a yankin Obajana na Jihar Kogi. Cikin waɗanda aka ceto akwai Sarkin Fulani na Asinwe a ƙaramar hukumar Okehi, wanda aka sace a gidansa, tare da wasu mutum huɗu da aka sace a ranar 12 ga Agusta, da kuma mutum biyu da aka sace a ranar 28 ga Yuli a Apata, Lokoja.

Kwamandan bataliya ta 12, kuma Kwamandan Operation Accord III, Birgediya Janar Kasim Sidi, wanda Commanding Officer na bataliya ta 126, Laftanar Kanal Francis Nwoffiah ya wakilta, ya ce an samu nasarar kuɓutar da fursunonin ne bayan samun sahihan bayanan leƙen asiri, inda dakarun suka bi sawun ƴan bindigar har cikin daji. Ya ce ƴan bindigar sun tsere da raunuka bayan fuskantar ƙarin ƙarfin Soji, suka bar waɗanda suka sace da kuma kayan su, ciki har da alburusai.

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata ’Yansanda Sun Gano Gawar Ɗan Jaridar Da Aka Kashe A Jihar Kogi

Ya ƙara da cewa, an kuɓutar da dukkan waɗanda aka sace ba tare da wani rauni ba, kuma za a haɗa su da iyalansu bayan sun sami kulawar likita. Janar Sidi ya gargaɗi ƴan ta’adda da masu garkuwa da mutane a Kogi da jihohin makwabta su tuba, in ba haka ba za su fuskanci mummunar sakamako.

Wani daga cikin waɗanda aka ceto, Sarkin Fulani na Asinwe, Malam Adamu Zage, ya gode wa Sojojin da sauran jami’an tsaro bisa jarumtar da suka nuna. Gwamnan jihar, Ahmed Usman Ododo, ya ce gwamnati ba za ta lamunci aikata laifuka a Kogi ba, tare da bayyana cewa ana ci gaba da kai farmaki kan masu aikata miyagun laifuka a jihar da kewaye.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sarkin Zuru: Muhammadu Sani Sami (1943-2025)
  • Amurka Ta Dakatar Da Bawa Falasdinawa A Gaza Visar Shiga kasar
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli
  • India Ta Dage Kan Maida martani da hana Shigowar Kayakin Amurka Kasar
  • Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Ya Kamata Japan Ta Martaba Tarihi
  • Sin Ta Soki Lamirin Amurka Dangane Da Wanke Japan Daga Laifukan Da Ta Tafka Yayin Yakin Duniya Na Biyu
  • Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi
  • Gwamnatin Mali Ta Bankado Wata Makarkashiyar Janyo Hargitsi A Kasar Tare Da Wargaza Shi
  • NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta
  • Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara