Wata majiya ta ce PDP na cikin mawuyacin hali da kuma rashin tabbas a harkokinta wanda ya tilasta jinkirta taron shiyya da aka shirya gudanarwa a karshen makon da ya gabata.

Wata majiya ta ce hukuncin da kotun koli ta zartar akwai rikitarwa saboda an gwama siyasa a ciki.

Amma sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na kasa, Debo Ologunagba ya fada a wata hira kan cewa hukuncin kotun koli a bayyane yake kuma yana da fa’ida ga gudanar da jam’iyyar a kasar, ya kara da cewa an ba da ikon magance matsalolin da ke tattare da rikice-rikicen da za su iya shafi masu rike da mukaman jam’iyyar.

Ya ce abin da kotun ta yanke hukunci shi ne cewa dole ne a warware duk wani abu da ya shafi matsayi na jam’iyya ta hanyar tsarin cikin gida na jam’iyya, sannan kotun ta ce ba za ta yi katsalandan ga al’amuran jam’iyyu ba kamar yadda dokoki da ka’idoji suka bayyana.

Ya ce PDP ba ta cikin wani mawuyacin hali game da hukuncin, ya kara da cewa tsarin cikin gida na jam’iyyar zai yanke shawara tare da samar da mafita.

Yayin da PDP tana cikin mawuyacin hali saboda jinkirin warware matsayin sakataren jam’iyyar na kasa, al’amura na kara tabarbarewa a LP. A makon da ya gabata ne bangare uku suke ikirarin zama shugabannin jam’iyyar na kasa.

Julius Abure, Nenadi Usman da Lamidi Apapa sun ci gaba ikirarinsu na zama a matsayin shugabancin jam’iyyar, duk da cewa sakataren yada labarai na kasa, Obiora Ifoh, ya bayyana cewa wadanda ke fafatawa da Abure suna yin was an kwaikoyo ne kawai.

A cewarsa, a yayin da kotun koli ta fadi karara cewa ba ta da iko a kan lamarin da ya shafi rikicin cikin gida na jam’iyya kuma ta mayar da iko ga tsarin jam’iyyar, wasu mambobin jam’iyyar suna yin wasan kwaikwayo ta hanyar zuwa ofishin hukumar zabe ta kasa, lamarin da ya ce ba shi da tasiri.

Ya ce hukuncin kotun koli ya yi watsi da batun shugabancin jam’iyyar tare da soke hukuncin kotun daukaka kara, har ma ba ta tabbatar da wani mutum a matsayin shugaban jam’iyyar ba.

“Abin da wannan ke nufi shi ne, an mayar da jam’iyyar zuwa matsayi na farko. Kuma Abure ya kasance shugaban jam’iyyar na kasa har tsawon lokacin da wa’adinsa ya kare,” in ji Ifoh.

Mai magana da yawun jam’iyyar ya gargadin Sanata Nenadi Usman da sauran masu adawa da Abure cewa kar su yaudari ‘yan Nijeriya da fassarar da ba daidai ba game da hukuncin kotun koli.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Dan Takarar Gwamnan PDP

এছাড়াও পড়ুন:

Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya mayar wa da Shugaban Amurka, Donald Trump martani cewa Najeriya ba ta yadda da duk wani nau’in zarafin addini.

Tinubu, ya yi wannan bayani ne bayan Trump ya sake sanya Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake kiran “Ƙasashen da ke da Babbar Matsala wajen ’Yancin Addini.”

PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa

Trump ya yi iƙirarin cewa Kiristoci a Najeriya na fuskantar barazana, amma ya sha alwashin cewa Amurka za ta kare su.

A cikin wani saƙo da ya wallafa a kafafen sada zumunta, Trump ya rubuta cewa: “Addinin Kirista yana fuskantar babbar barazana a Najeriya. Ana kashe dubban Kiristoci.”

A ranar Asabar, Tinubu ya mayar da martani ta kafar sada zumunta, inda ya ce Najeriya ƙasa ce mai dimokuraɗiyya wadda kundinta ya tabbatar da ’yancin yin addini.

“Najeriya tana da cikakken tanadi a kundinta da ya tabbatar da ’yancin yin addini,” in ji Tinubu.

“Tun daga shekarar 2023, gwamnatina na aiki tare da shugabannin Kiristoci da Musulmai don magance matsalolin tsaro da ke shafar jama’a daga kowane ɓangare da addini.”

Ya ƙara da cewa, kiran Najeriya ƙasa mai matsala wajen gudanar addini ba gaskiya ba ne.

“Za mu ci gaba da kare ’yancin kowane ɗan ƙasa na yin addininsa cikin walwala. Najeriya ba ta goyon bayan zaluncin addini ko kaɗan,” in ji Tinubu.

Ya kuma ce Najeriya za ta ci gaba da haɗa kai da Amurka da sauran ƙasashe domin inganta zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai daban-daban.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fursunan da aka yanke wa hukuncin kisa ya tsere daga gidan yari a Yobe
  • Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari
  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa