HausaTv:
2025-09-17@21:52:19 GMT

Iran Tace Yarjeniya Da Amurka Mai Yuwa Ne Idan Da Gaske Take

Published: 18th, April 2025 GMT

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa Iran zata halarci zaman tattaunawa da kasar Amurka kan shirin kasar na makamashin Nukliya tare da fatan bangaren Amurla ma tana bukatar cimma yarjeniya da ita, matukar Amurka bata kawo wani abu wand aba zai yu Iran ta amince ba.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan yana fadar haka a yau Jumma’a a birnin Mosco a lokacinda shi da tokwaransa na kasar Rasha Sergei Lavrov suke amsa tambayoyin yan jarida.

Ministan ya kara da cewa tawagarsa zata je taron birnin Roma tare da fatan tattaunawar zata yi kyau.

Ya kuma kara da cewa takunkuman tattalin arziki mafi muni wanda Amurka ta dorawa kasar da kuma yin kalamai biyu dangane da tattaunawa da kuma barazana da take wa JMI ba alamu ne na kekyawar niyyar Amurka  ba, amma zamu ci gaba da tattaunawar don ganin inda za’a itsaya.

A ranar Asabar 12 ga watan da Afrilun da muke ciki ne aka gudanar da tattaunawa tsakanin Iran da Amurka zagaye na farko a birnin Mascat na kasar Omman.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
  • Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha
  • An Fara Taron Hukumar Makamashin Nukliya Ta Duniya IAEA Karo Na 69 A Birnin Vienna
  • Ministan Tsaron Kasar venezuela Ya Gargadi Amurka Dangane Da Kokarin Juyin Mulki A Kasar
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai
  • Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
  • Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha
  • Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha