Iran Tace Yarjeniya Da Amurka Mai Yuwa Ne Idan Da Gaske Take
Published: 18th, April 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa Iran zata halarci zaman tattaunawa da kasar Amurka kan shirin kasar na makamashin Nukliya tare da fatan bangaren Amurla ma tana bukatar cimma yarjeniya da ita, matukar Amurka bata kawo wani abu wand aba zai yu Iran ta amince ba.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan yana fadar haka a yau Jumma’a a birnin Mosco a lokacinda shi da tokwaransa na kasar Rasha Sergei Lavrov suke amsa tambayoyin yan jarida.
Ministan ya kara da cewa tawagarsa zata je taron birnin Roma tare da fatan tattaunawar zata yi kyau.
Ya kuma kara da cewa takunkuman tattalin arziki mafi muni wanda Amurka ta dorawa kasar da kuma yin kalamai biyu dangane da tattaunawa da kuma barazana da take wa JMI ba alamu ne na kekyawar niyyar Amurka ba, amma zamu ci gaba da tattaunawar don ganin inda za’a itsaya.
A ranar Asabar 12 ga watan da Afrilun da muke ciki ne aka gudanar da tattaunawa tsakanin Iran da Amurka zagaye na farko a birnin Mascat na kasar Omman.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Araqchi: Iran Zata Mayar Da Martanin Da Ba Zai Yiwu A Boye Ba Kan Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kanta
Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Idan aka maimaita ta’asar kai hari kan Iran, za ta mayar da martani ta hanyar da ba za a iya boyewa ba
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya mayar da martani kan barazanar da jami’an Amurka suka yi a baya-bayan nan, inda ya ce idan aka sake kai hari kan Iran, za ta mayar da martani mai tsauri wanda ba zai yiwu a iya boye ba.
Araghchi ya kara da cewa a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter a ranar Litinin din nan cewa: Iran, kasar da ke da al’adun gargajiyar da ta shafe shekaru dubu bakwai na wayewar kai, ba za ta taba mika kai ga barazana da tsoratarwa ba. Iraniyawa ba su taba mika kai ga kasashen waje ba kuma ba su bukatar komai sai girmamawa.
Ya ci gaba da cewa: “Iran ta san hakikanin abin da aka yi mata da kuma abin da makiya suka fuskanta a lokacin farmakin da ‘yan sahayoniyya da Amurka suka yi a baya-bayan nan, ciki har da yawan munanan hare-haren da ta kai a matsayin daukan fansa wadanda ake ci gaba da boyewa. Don haka idan makiya suka sake kuskuren kai hari kan Iran, babu shakka zasu fuskanci martani mai gauni da ba zai yiwu a iya boyewa ba.