Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi kira ga al’ummar duniya da su ba da himma wajen shiga wani gangami na tsawon mako guda domin ganin an kawo karshen mummunan yakin da Isra’ila ke yi na kisan kiyashi a zirin Gaza da aka yi wa kawanya.

A cikin wata sanarwa da ta fitar yau Laraba, Hamas ta yi kira ga “kasashen Larabawa da na musulmi da kuma ‘yantattun mutane” na duniya da su halarci gangamin na ranakun Juma’a, Asabar da Lahadi (18, 19 da 20 ga Afrilu).

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinu ta ayyana wadannan ranaku a matsayin “ranakun nuna fushin duniya dangane da mamaya.”

Hamas ta sake nanata bukatar daukar matakin gaggawa na kasa da kasa don kawo karshen “ci gaba da cin zarafi da kisan kiyashin da yahudawan sahyoniya suka yi wa al’ummar Falasdinawa a Gaza, wanda ke gudana a karkashin goyon bayan Amurka da kuma shiru na kasa da kasa.”

Har ila yau, ta yi kira da a gudanar da yajin aikin gama-gari a ranar Talata 22 ga watan Afrilu a dukkan jami’o’i da cibiyoyin ilimi na duniya domin tallafawa al’ummar Gaza da aka yi wa kawanya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴan Ta’adda Sun Kashe Maharba 10 A Adamawa

Ƴan ta’adda da ake zargin Boko Haram ne sun kashe mutane 10 na yawucin dabbobi da kuma mambobin jami’an tsaron sa kai (CJTF) a garin Kwapre, dake cikin ƙaramar hukuma ta Hong a Jihar Adamawa.

Shugaban ƙaramar hukuma, Hon Usman Wa’aganda, ya tabbatar da wannan lamarin ga LEADERSHIP ta waya a ranar Lahadi a Yola, inda ya bayyana cewa wani mutum da ya samu raunuka daga harin ‘yan ta’addan yana samun kulawar likita a wani asibiti da ba a bayyana sunansa ba.

Daidaikun Kasashe Za Su Kara Karfi Idan Suka Hada Hannu Tare ‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa

Wa’aganda ya ce ‘yan ta’addan sun ƙone gidaje da dama da kuma amfanin gona, yana mai cewa wannan harin ba na farko bane, domin garin ya sha hare-hare sau da dama wanda ya haifar da asarar rayuka da dukiyoyi.

Ya nemi hukumomin tsaro su ƙara tura jami’ai a yankin domin taimakawa wajen kare al’umma da kuma tabbatar da tsaro.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Saudiya Ta Yi Allawadai Da Kissan Kiyashin Da HKI Take Yi A Gaza A Gaban Kutun ICJ
  • Kungiyar Amnesty International Ta Kafa Hujja Kan Ta’asar’Yan Sahayoniyya A Gaza
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Shin Amurka Na Iya Komawa Kan Kadaminta A Matsayin Cibiyar Masana’antun Duniya?
  • Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran
  • Lebanon:  Isra’ila Ta Kai Hari Akan Unguwar Dhahiya A Birnin Beirut
  • Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar
  • Ƴan Ta’adda Sun Kashe Maharba 10 A Adamawa
  • Daidaikun Kasashe Za Su Kara Karfi Idan Suka Hada Hannu Tare