Kamata Ya Yi Amurka Ta Kara Kokarin Gyara Kuskurenta
Published: 15th, April 2025 GMT
Wasu kafofin yada labarai a duniya na ganin cewa, idan gwamnatin Amurka ta ci gaba da saka shingayen haraji, to sauran kasashe za su maye gurbinta a bangaren samar da hidimomi. Abin da gwamnatin ta yi biris da shi yayin da take kididdigar harajin da za ta kakabawa sauran sassa, har yanzu wannan bangare na shiga gogayyar ciniki.
Bisa bayyanan da aka fitar, Amurka ta dade tana cin rarar kudin ciniki a bangaren ba da hidimomi. Alal misali a shekarar 2024, yawan rarar kudin da ta samu a wannan bangare ya kai dala biliyan 300. Kuma Abin lura shi ne, cinikin hidimomi na matukar dogaro da cinikin kayayyaki. Gibin kudin cinikin da Amurka ta samu a bangaren cinikin kayayyaki da rarar kudin cinikin da ta samu ta fuskar cinikin hidimomi, ya faru ne bayan sauyin salon sana’o’i bisa matakai daban daban, ta yadda suka kasance tagwaye da ba za a iya raba su ba.
Idan an yi waiwaye kan tushen cinikin hidimomi wato batun amincewa, a wadannan shekaru da suka gabata, Amurka ta rika sanya takunkumai da haifar da barazana ga dukkanin fadin duniya, wanda hakan ya rage kimarta, da amincewa daga sauran kasashe. A halin yanzu, Amurka ta kakabawa sauran kasashe harajin kwastam yadda take so, kuma abun tambaya shi ne wa zai karbi hidimomin da Amurka za ta samar a bangaren hada-hadar kudi, da ba da ilmi da bayanai da kuma kwamfuta?
Amurka ita kanta za ta dau laifin gogayyar ciniki, matakin da ta dauka a wannan karo na kawar da harajin kwastam na ramuwar gayya kan wasu kayayyaki, dabara ce ta kubutar da kanta daga mawuyacin hali. Amma, hakan bai wadatar ba, dole ne ta dauki karin matakai na soke dukkanin wannan haraji da ta kakabawa sauran kasashe. A wani bangare kuwa, ta mutunta abokan cinikinta, ta yi shawarwari da su bisa adalci da daidaito, a matsayin hanya daya tilo mafi dacewa da za ta bi wajen warware bambancin ra’ayi na ciniki. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: sauran kasashe
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Najeriya Wajen Yin Watsi Da Kariyar Cinikayya Da Yin Adawa Da Danniya Da Cin Zarafi
Haka kuma Wang ya halarci taron ministocin waje na kasashe mambobin kungiyar BRICS da na kasashe kawayensu a wannan rana, inda aka tattauna game da yadda za a karfafa ra’ayin cudanyar bangarori daban daban.
Wang ya bayyana cewa, mafitar matsalolin da ake fuskanta a duniya ita ce kiyayewa da aiwatar da ra’ayin cudanyar bangarori daban daban. Ya ce bayan da ta habaka mambobinta, ya kamata kungiyar BRICS ta ci gaba yayata manufar yin shawarwari da juna da tabbatar da ci gaban juna da cin moriya tare, da kiyaye muhimman ka’idojin huldar kasa da kasa, da kuma kare tsarin ciniki tsakanin bangarori daban daban.
Wang ya jadadda cewa, amsar da Sin ta bayar game da yakin cinikayya a bayyane take, wato idan an dage kan yakin, ko kadan ba za mu ja da baya ba. Idan an shirya tattaunawa, dole ne mu girmama juna tare da yin zaman daidaito da juna. Ba don hakkinta na kanta ba ne, kasar Sin tana kuma kiyaye muradun bai daya na dukkanin kasashe. Abun da kasar Sin ke kiyayewa ba kawai hadin gwiwar cin moriyar juna ba ne, har ma da ka’idojin kasa da kasa. (Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp