A cewarsa, wadannan kudaden sun hada da biyan kudaden samar da kariya da na inshore da kuma sauran kudaden da ake biyan kamfanonin na waje.

Ya sanar da cewa, wadanan kudaden da ake biya, na shafar ci gaban tattalun arzikin kasar, inda ya yi nuni da cewa, duk Jirgin ruwa daya da ya yi dakon Danyen Mai ana biyan dala miliyan 130, inda kuma ake cazar kudin da suka kai akalla dala 445,000.

Kazalika, Osagie ya bayyana cewa, ana jigilar Kwantaina kuma ana biyan dala miliyan $150, wanda kuma ake cazar dala 525,000, kan kowacce jigila daya.

Kamfanin Maersk, daya daga cikin manyan kamfanoni a duniya da ke dakon kaya, ya kirkiro kowacce Kwantaina na biyan dala 450, wanda kuma yake cazar daga dala 40 zuwa dala 50 a kan Kwantaina 20.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Rage Farashin Man Fetur Na Dangote Ya Sa Wasu Gidajen Mai Na Kullewa

“Saboda ragin farashin litar man fetur da Dangote ya yi ne. Gidan man yana da tsohon mai da ya saya a farashin da ya fi wannan, kuma ba zai sayar da shi a asara ba.

 

“Wannan dalilin ne ya sanya muka rufe gidajen man tun ranar Talata. Da yiwuwar mu bude nan gaba.”

 

Kazalika, wani ma’aikacin gidan man, ya tabbatar da cewa suna ‘yan wasu gyare-gyare ne amma za su sake budewa. Ya kuma ce, gidan man zai fara sayar da man fetur ga jama’a a ranar Talata kan kudi naira 910 a kowace lita.

 

Rahotonni sun tabbatar da cewa sauran abokan huldar matatar man Dangote, kamar su AP, Ardoba, da Optima, sun yi ta sayar wa jama’a da fitar kan kudi tsakanin naira 910 zuwa 920 kan lita guda a wasu sassan Abuja zuwa ranar Litinin da ta gabata.

 

Da yake tofa albarkacin bakinsa kan wannan lamarin, shugaban kungiyar Dillalan Mai a Nijeriya, Billy Gillis-Harry, ya ce, saukan farashin man fetur ya shafi karfin sayen mai na dillalai da ‘yan kasuwa.

 

A cewarsa, yawan sauka da tashin farashin mai ba abu ne mai dadi ga sashin mai da kuma tattalin arzikin Nijeriya ba, “Ba abu ne mai kyau ga kasuwanci da tattalin arziki da ma ‘yan Nijeriya ba.”

 

A baya dai Gillis-Harry ya taba yin kiran da a shafe sama da watanni shida a kan farashin fetur ba tare da canji ba domin kyautata harkokin kasuwancinsa.

 

Shi kuma mai magana da yawun kungiyar masu gidajen mai masu zaman kansu (IPMAN), Chinedu Ukadike, ya ce masu gidajen mai suna da fetur da suka sayo a tsohon farashi ne, kuma matakin matatar Dangote na rage farashin zai sanya su tafka asarar biliyoyin naira.

 

A baya-bayan nan ne Kamfanin Man Fetur na Nijeriya ya rage farashin ga dillalansa zuwa naira 935 ga kwastomomi a Abuja a matsayin martani ga sabon rage farashin matatar man Dangote.

 

Hakan na nufin a halin yanzu ‘yan Nijeriya na sayen man fetur a tsakanin naira 890 zuwa naira 950 kan kowace lita.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Manyan Bankuna 5 Da Suka Samu Ribar Naira Tiriliyan 17.3 A Nijeriya
  • Mahaifi ya kashe ɗansa mai shekara 6 don yin tsafi a Gombe
  • Rage Farashin Man Fetur Na Dangote Ya Sa Wasu Gidajen Mai Na Kullewa
  • Kudaden Da Ke Hannun Mutane Sun Ragu Zuwa Naira Tiriliyan 5 – Rahoto
  • Sharhin Bayan Labarai: Shin Kissan Mutanen Gaza Gaba Daya
  • An Umurci Sojoji Su Kawarda ‘Yan Bindiga Daga Kwara Da Niger A Cikin Wata Daya
  • Majalisun jihohi sun buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro
  • Mahmuda: Sabuwar ƙungiyar ’yan ta’adda ta ɓulla a Nijeriya
  • Sabbin Haraji: Yadda ‘Yan Bindiga Ke Tilasta Wa Jama’a Biyan Miliyoyin Kuɗi A Zamfara
  • ’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi