Aminiya:
2025-09-17@21:48:51 GMT

Trust Radio 92.7FM za ta fara shirye-shiryen gwaji

Published: 10th, April 2025 GMT

Kamfanin Media Trust Limited na farin cikin sanar da al’umma cewa daga ranar Juma’a 11 ga watan Afrilun 2025, Rediyonta na Tusts Radio zai fara shirye-shiryen gwaji.

Tashar za ta fara yaɗa shirye-shiryenta a kan mita 92.7 a zangon FM a birnin tarayya Abuja da kewaye, kuma wannan na daga cikin tsare-tsaren da kamfanin ke bi na faɗaɗa aikin watsa labarai sama da shekaru 27 a Nijeriya.

An kama masu garkuwa da mutane biyu a Yobe Gwamnatin Kano ta tura tawaga zuwa Edo kan kisan mafarauta

Kamfanin Media Trust shi ne mai wallafa jaridun Daily Trust da Aminiya a Nijeriya kuma mamallakin Trust TV da kuma Trust Radio a yanzu.

Ga waxanda ba su a birnin tarayya Abuja ko kuma suka yi tafiya za su iya kama tashar a shafinta na intanet a https://trustradio.com.ng ko a manhajar Radio Garden.

Haka kuma za a iya saurarenta shafukan Aminiya da Daily Trust da shafukan sada zumunta.

Da zarar tashar ta kammala gwajin za ta fara watsa ƙayatattun shirye-shirye da labarai tare da rahotanni masu ilimantarwa, faxakarwa tare da nishaɗantarwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Trust Radio shirye shirye

এছাড়াও পড়ুন:

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sun jaddada cewa dole ne manyan kafafen sada zumunta su kare ‘yancin yin magana.

Sun kuma yi kira ga ‘yan Nijeriya, ‘yan jarida, da masu fafutukar kare haƙƙin bil’adama su tashi tsaye don hana abin da suka kira yunƙurin mayar da Nijeriya “mulkin kama-karya a intanet.”

Lamarin ya biyo bayan wa’adin sati guda da DSS ta bai wa Sowore da ya goge wasu wasu rubuce-rubuce game da Shugaba Bola Tinubu, wanda ya ƙi amincewa.

Hakan ya sa hukumar ta shigar da shi ƙara a kotu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaidai Dake Kasar Yamen
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara