Aminiya:
2025-04-30@19:46:51 GMT

An kama masu garkuwa da mutane biyu a Yobe

Published: 10th, April 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Yobe ta samu gagarumar nasara a ƙoƙarinta na yaƙi da miyagun laifuka, inda ta cafke wasu fitattun mutane biyu da ake zargi da garkuwa da mutane.

Waɗanda aka kama sun haɗa da: Babaro Baushe mai kimanin shekara 40 da Umaru Dau’a, mai kimanin shekara 25 da suka fito daga ƙauyen Askuwari a ƙaramar hukumar Tarmuwa a ranar 9 ga Afrilu, 2025.

Gwamnatin Kano ta tura tawaga zuwa Edo kan kisan mafarauta Ruwan sama ya lalata gidaje da yawa a Kebbi

A takardar sanarwar da kakakin rundunar ‘Yan sandan Yobe, SP Dungus Abdulkareem ya fitar ya ce, hedikwatar ’yan sanda reshen Dapchi da misalin ƙarfe 0500hrs, 9 ga Afrilu, 2025, ta cafke waɗanda ake zargin, ’yan ƙungiyar da suka ƙware wajen yin garkuwa da mutane domin neman kuɗin fansa da kuma neman barace-barace, suna gudanar da ayyukansu a ƙananan hukumomin Dapchi da Tarmuwa.

An dai alaƙanta waɗanda ake zargin da laifuka da dama da suka haɗa da: A ranar 21 ga Nuwamba, 2024, masu garkuwar sun kai hari ƙauyen Badegana da kuma kai hari gidan wani da aka kashe, wanda ya yi sanadin rasa rai.

A ranar 10 ga Maris, 2025, waɗanda ake zargin sun karɓe N250,000 da ƙarfi daga Mudi Ibrahim na ƙauyen Askuwari, ƙaramar hukumar Tarmuwa, bayan sun yi barazanar sace shi ko kuma su kashe shi.

Waɗannan mutane sun amsa laifukan da suka aikata, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike a sashin bincike na jihar (SID).

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Emmanuel Ado  ya ba da umarnin ci gaba da ƙoƙarin kama wasu ’yan ƙungiyar kuma ya buƙaci al’umma da su bayar da sahihan bayanai don taimakawa wajen gudanar da bincike.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Tarmuwa yan sandan

এছাড়াও পড়ুন:

Talauci Da Rashin Ilimi Ne Ya Sa Ayyukan Boko Haram Ke Dawowa – Gwamnan Yobe

Shugaban tawagar baƙin, Alhaji Ibrahim Abdullahi Yar’adua, ya ce sun zo Yobe domin nazarin halin tsaro da tattara bayanai da za su taimaka wajen tsara manufofin tsaron ƙasa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  • Talauci Da Rashin Ilimi Ne Ya Sa Ayyukan Boko Haram Ke Dawowa – Gwamnan Yobe
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • Sojoji Sun Harbe Mutane Biyu Har Lahira Da Ake Zargi Ɓarayin Mota Ne A Filato 
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Sama Da Masu Sayayya Daga Ketare 220,000 Ne Suka Halarci Bikin Baje Kolin Canton Karo Na 137
  • Aikin Hajji: Za A Fara Jigilar Alhazan Jihar Kwara A Ranar 12 Ga Watan Mayu
  • Jagora Ya Bada Umurnin A Gudanar Bincike Mai Zurfi A Fashewar Tashar Jiragen Ruwa Na Shaheed Rajae