Aminiya:
2025-09-17@23:30:17 GMT

Mutanen da suka saba ba ni abinci yanzu na neman taimako — Obi

Published: 9th, April 2025 GMT

Ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023, Peter Obi, ya ce talauci a Najeriya ya tsananta matuƙa har ta kai mutanen da suka saba ba shi abinci a baya yanzu suna neman taimako daga wajensa.

Obi, ya bayyana hakan ne a lokacin taron kwamitin zartarwa na ƙasa na jam’iyyar LP da aka gudanar a otal ɗin Transcorp Hilton da ke Abuja a ranar Laraba.

Bai wa ’yan bindiga kuɗin fansa na dagula sha’anin tsaro — Ribadu Harajin China da Amurka: Mece ce makomar tattalin arziƙin duniya?

“Najeriya na rushewa. Lamarin tattalin arziƙi na ƙara taɓarɓarewa, mutane na ƙara shiga cikin talauci kullum,” in ji Obi.

“Ya kamata mu riƙa magana idan abubuwa ba sa tafiya daidai. Ka da mu ji tsoro. Waɗanda suka ji tsoro a baya, ba su yi wani abu mai amfani ba.”

Ya ce jam’iyyarsu tana shirya shiga babban zaɓen mai zuwa, inda za su fito da ‘yan takara masu nagarta da ƙwarewa daga matakin Majalisar Wakilai, Sanatoci, Gwamnoni har zuwa Shugaban Ƙasa.

Obi, ya kuma ƙaryata jita-jitar cewa yana shirin barin jam’iyyar LP tare da komawa wata jam’iyyar.

Ya ce bai tattauna da kowa ko wani ƙungiya kan ficewarsa daga jam’iyyar ba, kuma duk wani abu da za a yanke game da makomar jam’iyyar, za a yi ne tare da sauran mambobinta.

“Ban taɓa cewa zan bar jam’iyyar LP ba,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Matsin Rayuwa Tattalin Arziƙi

এছাড়াও পড়ুন:

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Kafin ya zama mataimakin shugaban jam’iyyar APC, Barde ya taɓa zama Shugaban riƙo na Karamar Hukumar Wamba a zamanin tsohon Gwamnan Jihar Umaru Tanko Al-Makura.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
  • NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025
  • Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
  • An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000