Aminiya:
2025-11-03@00:16:29 GMT

Mutanen da suka saba ba ni abinci yanzu na neman taimako — Obi

Published: 9th, April 2025 GMT

Ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023, Peter Obi, ya ce talauci a Najeriya ya tsananta matuƙa har ta kai mutanen da suka saba ba shi abinci a baya yanzu suna neman taimako daga wajensa.

Obi, ya bayyana hakan ne a lokacin taron kwamitin zartarwa na ƙasa na jam’iyyar LP da aka gudanar a otal ɗin Transcorp Hilton da ke Abuja a ranar Laraba.

Bai wa ’yan bindiga kuɗin fansa na dagula sha’anin tsaro — Ribadu Harajin China da Amurka: Mece ce makomar tattalin arziƙin duniya?

“Najeriya na rushewa. Lamarin tattalin arziƙi na ƙara taɓarɓarewa, mutane na ƙara shiga cikin talauci kullum,” in ji Obi.

“Ya kamata mu riƙa magana idan abubuwa ba sa tafiya daidai. Ka da mu ji tsoro. Waɗanda suka ji tsoro a baya, ba su yi wani abu mai amfani ba.”

Ya ce jam’iyyarsu tana shirya shiga babban zaɓen mai zuwa, inda za su fito da ‘yan takara masu nagarta da ƙwarewa daga matakin Majalisar Wakilai, Sanatoci, Gwamnoni har zuwa Shugaban Ƙasa.

Obi, ya kuma ƙaryata jita-jitar cewa yana shirin barin jam’iyyar LP tare da komawa wata jam’iyyar.

Ya ce bai tattauna da kowa ko wani ƙungiya kan ficewarsa daga jam’iyyar ba, kuma duk wani abu da za a yanke game da makomar jam’iyyar, za a yi ne tare da sauran mambobinta.

“Ban taɓa cewa zan bar jam’iyyar LP ba,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Matsin Rayuwa Tattalin Arziƙi

এছাড়াও পড়ুন:

Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan

Jamus ta shiga sahun ƙasashen duniya da ke kiran a gaggauta tsagaita wuta a yaƙin da ke ci gaba da salwantar rayuka a ƙasar Sudan.

Sama da shekaru biyu ke nan Sudan na fama da yaƙin da ya ɗaiɗaita fararen hula baya ga asarar rayuka.

Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump

Ministan Harkokin Wajen Jamus, Johann Wadephul, ya bayyana halin da Sudan ke ciki a matsayin “mummunan bala’i,” yana mai cewa babbar matsalar jinkai ta duniya a yanzu ta tattara ne a Sudan ɗin.

A taron da aka gudanar a Bahrain, ƙasashen Birtaniya da Jordan su ma sun yi magana kan rikicin, suna kiran da a kawo ƙarshen tashin hankalin.

A ƙarshen makon da ya gabata, RSF ta kori rundunar soji daga sansanin ta na ƙarshe a yammacin Darfur.

Rahotanni daga garin El-Fasher sun bayyana cewa ana samun kashe-kashe ba tare da shari’a ba, da fyaɗe da fashi har ma da hare-hare kan ma’aikatan agaji.

Wata Kungiyar Likitoci ta MSF a ranar Asabar ta ce ana fargabar dubban fararen hula sun maƙale sannan suna cikin mummunan haɗari a birnin Al Fasher wanda ya koma hannun dakarun RSF.

Rikicin Sudan ya fara ne a watan Afrilun 2023, bayan taƙaddama ta siyasa tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan, shugaban sojin ƙasar, da Mohamed Hamdan Dagalo (Hemedti), Kwamandan RSF.

Bayanai sun ce rikicin ya samo asali ne daga saɓani kan yadda za a haɗa rundunar RSF da sojojin ƙasar bayan juyin mulkin 2021 da ya hamɓarar da gwamnatin farar hula.

Tun daga lokacin, yaƙin ya zama wani mummunan bala’i na jin kai, inda Majalisar Ɗinkin Duniya (UN) ta ce fiye da mutane miliyan bakwai sun tsere daga gidajensu, yayin da dubbai ke buƙatar taimakon gaggawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan
  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure