Aminiya:
2025-08-01@01:55:33 GMT

Harajin China da Amurka: Mece ce makomar tattalin arziƙin duniya?

Published: 9th, April 2025 GMT

Sabon rikici ya sake kunno kai tsakanin ƙasashen China da Amurka, yayin da shugaba Donald Trump, ya ƙara wa kayayyakin da ake shiga da su ƙasar daga China haraji zuwa kashi 104.

Wannan matakin ya shafi kayayyaki kamar wayoyin hannu, batir, kayan wasan yara da na’urorin wasanni.

Za a ci gaba da sayar da ɗanyen mai a farashin Naira — Gwamnati  Likitocin Nijeriya dubu 16 sun yi ƙaura zuwa ƙetare — Ministan Lafiya China ta ce ba za ta zuba ido ba

China ta bayyana cewa ba za ta zuba ido ta yi tagumi yayin da ake gallaza mata.

China ta mayar da martani da nata harajin kashi wanda ta ƙada zuwa kashi 34 kan kayayyakin Amurka, inda ta kuma ce tana shirin ƙara wani harajin.

Ta rage darajar kuɗinta (Yuan) domin ƙarfafa fitar da kayayyaki zuwa ƙasashen waje.

A lokaci guda kuma, ta fara bincike kan wasu manyan kamfanonin Amurka kamar Google, inda kuma ta ke shirin daƙile wasu muhimman albarkatu.

Masana tattalin arziƙi na gargaɗin cewa wannan rikici zai shafi ƙasashe da dama, musamman na nahiyar Asiya kamar Vietnam da Cambodia, waɗanda harajin zai shafa daga Amurka.

Ana kuma ganin cewa wannan zai iya janyo hauhawar farashin kayayyaki a Amurka da kuma raguwar sayayya daga China.

Wannan ba rikicin haraji ba ne – Ƙwararru

Wasu ƙwararru sun bayyana cewa wannan ba kawai rikicin haraji ba ne, wata gwagwarmaya ce ta nuna iko a harkokin kasuwancin duniya.

Ko da yake tattalin arziƙin China na fuskantar tangarɗa a yanzu, amma masana na ganin tana iya ɗorewa, domin kauce wa nuna rauni ga matakin da Amurka ke kai mata.

A gefe guda kuwa, Amurka na fama da matsin lamba daga ‘yan kasuwa da masu zuba jari da ke jin tsoron sakamakon wannan rikici.

Masana na fargabar lokacin da rikicin zai ƙare

Masana sun bayyana cewa da wuya a san yadda wannan rikici zai ƙare.

Amma ana fatan cewa shugabannin ƙasashen biyu za su zauna tattaunawa domin samun mafita.

Ƙasashen duniya na fargabar cewa idan ba a daidaita ba, rikicin na iya taɓa tattalin arzikin duniya gaba ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: duniya Haraji Tattalin Arziƙi

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah

Gwamnatin kasar Amurka ta umurci gwamnatin kasar Lebanon ta kwance damarar kungiyar Hizbullah a kudancin kasar ko kuma ba zata sake maganar tattaunawa da gwamnatin kasar kan samuwar sojojin HKI a wurare 5 a kudancin kasar ba, ko kuma maganar HKI ta dakatar da hare hare a kan kasar ba.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa bayyana cewa dole gwamnatin kasar Lebanon ta kwamce damarar hizbullah .

A kwanakin baya gwamnatin Amurka ta bawa gwamnatin kasar Lebanon zuwa karshen wannan shekarar ko ta kwance damarar kungiyar Hizbullah ko kuma HKI na da damar yin abinda taga dama da kasar Lebanon.

A wani bangare kuma shugaban majalisar dokokin kasar Lebanon Nabi Beri ya tabbatar da cewa matukar HKI bata dabbaka yarjeniyar da aka cimma da ita a lokacin tsagaita budewa juna wuta ba.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku July 30, 2025  Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kada Yankin Kamtashatka Na Kasar Rasha July 30, 2025  Yahudawa ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Cikin Masallacin Kudus July 30, 2025 Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka July 30, 2025 Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu July 30, 2025 Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu July 30, 2025 MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya July 30, 2025 Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba July 30, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami July 30, 2025 Faransa Ta Bayyana Wuce Gona Da Irin ‘Yan Sahayoniyya Kan Falasdinawa Da Ayyukan Ta’addanci July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah
  • Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
  • Shugabannin Arewa Sun Tattauna Sabon Hanyar Ci Gaba – Minista Uba Maigari Ya Yaba
  • Za mu halasta kafa ƙasar Falasɗinu muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba — Birtaniya
  • Muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba za mu amince da kafa ƙasar Falasɗinu — Birtaniya
  • Ambaliya ta yi ajalin mutum 30 a China