Limamin Pangu Gari Ya Nemi Gwamnan Neja Ya Sanya Baki Kan Rikicin Fili A Yankin
Published: 9th, April 2025 GMT
An yi kira ga Gwamna Mohammed Umar Bago na jihar Neja da ya sanya baki kan rikicin fili mai fadin sama da hektar saba’in da biyar da ake zargin Hakimin Tegina da ke karamar hukumar Rafi ya kwace daga hannun mamallakinsa a Pangu Gari.
Babban Limamin Pangu Gari, Alhaji Umar Musa Danladi ne ya yi wannan kiran yayin da yake zantawa da manema labarai a Minna, inda ya bayyana cewa hakan yana da muhimmanci matuka, domin dakile rikicin da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin.
Alhaji Umar Musa Danladi ya bayyana cewa ya gaji filin gonar ne daga mahaifinsa wanda ya rasu kusan shekaru goma da suka gabata, kuma yana da burin barin filin ga ‘ya’yansa su gada.
Babban Limamin ya bayyana cewa wata kotun Shari’a da ke yankin ta shiga tsakaninsa da wani mutum da ya gina shago a cikin filin, haka kuma ya ci nasara a wata kara da ke dauke da lamba SC/Teg/Cr_25/2024 da ya shigar kan Hakimin Tegina da wasu mutum bakwai a bara.
A cewarsa, ci gaba da cin zarafin da Hakimin Tegina, Alhaji Garba Bako ke yi masa, wani abu ne da ke nuna raina kotu, wanda ya kamata a dauki mataki cikin gaggawa domin samar da zaman lafiya mai dorewa bisa ka’idojin adalci, da gaskiya da gudanar da aiki da nagarta da gwamnatin Gwamna Mohammed Umar Bago ke tsayawa a kai.
Sai dai ya zargi Hakimin Tegina, Alhaji Garba Bako, da cewa ya bayar da wani yanki na filin gonar nasa ga wasu manoma domin su noma, tare da umartar jami’an tsaro su kama Babban Limamin Pangu Gari da duk wani dan uwansa da aka gani a filin gonar.
Alhaji Musa Umar Danladi ya kuma nemi Sarkin Kagara, Alhaji Attahiru Gunna na biyu wanda ya bayyana a matsayin masoyin zaman lafiya, da ya kara shiga tsakani a rikicin filin gonar domin ya samun abin da ya ce mallakinsa ne na hakika.
Ya kuma bukaci ‘yan uwansa su ci gaba da kasancewa cikin zaman lafiya tare da jiran amsa mai kyau da shiga tsakani daga bakin Gwamnan Jihar Neja da kuma Sarkin Kagara, wadanda ya bayyana a matsayin mutane masu gaskiya da adalci akan aikinsu.
Daga Aliyu Lawa
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: zaman lafiya filin gonar
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Duk wani harin wuce gona da iri kan Iran zai fuskanci mayar da martani daidai da shi cikin gaggawa
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya tabbatar da cewa Iran na da kwarin gwiwa kan iya dakile duk wani yunkuri da wasu bangarorin ke yi na kawo cikas ga manufofinta na ketare.
Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araqchi ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa: Rudun gwamnatin yahudawan sahayoniyya, wadda take ganin za ta iya gindaya wa Iran abin da ya kamata ko kuma bai kamata ba, rudun tunani ne da ya yi nesa da hakikanin gaskiya, ta yadda bai cancanci mayar da martani ba.
Araqchi ya kara da cewa: “Duk da haka, jajircewar Netanyahu wani abin lura ne, a yayin da yake kokarin neman bayyana wa Shugaba Trump abin da zai iya ko kuma ba zai iya yi a diflomasiyyarsa da Iran ba!”
Ministan harkokin wajen ya yi nuni da cewa: “Abokanan Netanyahu a cikin tawagar Biden da ta gaza – wadanda suka kitsa makarkashiyar hana cimma yarjejeniya da Iran – suna kokarin nuna zaman tattaunawar da ake yi ba na kai tsaye ba da gwamnatin Trump a matsayin wani kuskure ne kuma tamkar hoton sauran yarjejeniyar nukiliya ce da aka gudanar.”