An yi kira ga Gwamna Mohammed Umar Bago na jihar Neja da ya sanya baki kan rikicin fili mai fadin sama da hektar saba’in da biyar da ake zargin Hakimin Tegina da ke karamar hukumar Rafi ya kwace daga hannun mamallakinsa a Pangu Gari.

 

Babban Limamin Pangu Gari, Alhaji Umar Musa Danladi ne ya yi wannan kiran yayin da yake zantawa da manema labarai  a Minna, inda ya bayyana cewa hakan yana da muhimmanci matuka,  domin dakile  rikicin da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin.

 

Alhaji Umar Musa Danladi ya bayyana cewa ya gaji filin gonar ne daga mahaifinsa wanda ya rasu kusan shekaru goma da suka gabata, kuma yana da burin barin filin ga ‘ya’yansa su gada.

 

Babban Limamin ya bayyana cewa  wata kotun Shari’a da ke yankin  ta shiga tsakaninsa da wani mutum da ya gina shago a cikin filin, haka kuma ya ci nasara a wata kara da ke dauke da lamba SC/Teg/Cr_25/2024 da ya shigar kan  Hakimin Tegina da wasu mutum bakwai a bara.

 

A cewarsa, ci gaba da cin zarafin da Hakimin Tegina, Alhaji Garba Bako ke yi masa, wani abu ne da ke nuna raina kotu, wanda ya kamata a dauki mataki cikin gaggawa domin samar da zaman lafiya mai dorewa bisa ka’idojin adalci, da gaskiya da gudanar da aiki da nagarta da gwamnatin Gwamna Mohammed Umar Bago ke tsayawa a kai.

 

Sai dai ya zargi Hakimin Tegina, Alhaji Garba Bako, da cewa ya bayar da wani yanki na filin gonar nasa ga wasu manoma domin su noma, tare da umartar jami’an tsaro su kama Babban Limamin Pangu Gari da duk wani dan uwansa da aka gani a filin gonar.

 

Alhaji Musa Umar Danladi ya kuma nemi Sarkin Kagara, Alhaji Attahiru Gunna na biyu wanda ya bayyana a matsayin masoyin zaman lafiya, da ya kara shiga tsakani a rikicin filin gonar domin ya samun abin da ya ce mallakinsa ne na hakika.

 

Ya kuma bukaci ‘yan uwansa su ci gaba da kasancewa cikin zaman lafiya tare da jiran amsa mai kyau da shiga tsakani daga bakin Gwamnan Jihar Neja da kuma Sarkin Kagara, wadanda ya bayyana a matsayin mutane masu gaskiya da adalci akan aikinsu.

 

Daga Aliyu Lawa

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: zaman lafiya filin gonar

এছাড়াও পড়ুন:

Mutanen Sweida Na Kasar Siriya Suna Fama da Rashin Abinci da Ruwa

A yankin sweida na kudancin kasar Siriya mazauna wurin sun bayyana cewa abinci da ruwa da kuma kayakin bukatu nay au da kullum sun fara karanci sosai a yankin saboda yakin makonni uku da suke fafatawa da sojojin sabuwar gwamnati a Damascus.

Jaridar The National ta Amurka ta bayyana cewa yankin sweida na kudancin kasar Siriya wanda kuma HKI ta dade tana shigowa yankin ta fita a halin nyanzu yana fama da karancin abinci da ruwansha. Sannan da alamun har yanzun sojojin sabuwar gwamnatin kasar Siriya tana ci gaba da hana shigowar abinci da ruwa yankin duk tare da shelanta tsagaita wuta da aka yi.

Labarin ya kara da cewa. an kashe daruruwan mutane a fafatawar da mayakan hTI suka yi da drsawa da suka fi rinjaye a yankin da kuma wasu kananan kabilu a yankin.

Tun lokacinda HKI tare da taimakin kasashen turkiya da sauran kasashen yamma suka kifar da gwamnatin Bashar al-asad, kasar Siriya take fama da karin kashe-kashe na kabilanci da na addini a kasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami
  • Kwamitin Aikin Hajjin 2025 Na Jihar Kano Ya Kammala Rahoton Aikinsa Na Wucin Gadi
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata 
  • Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci
  • Mutanen Sweida Na Kasar Siriya Suna Fama da Rashin Abinci da Ruwa
  • Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutumin Da Ake Tuhuma Da Safarar Miyagun Kwayoyi
  • Wulayati: Hanyar Zangezur Wata Shirin Amurka Ne Don Matsa lamba Kan Iran Da Rasha                                                                                                                       
  • Wulayati: Hanyar Zangezur Wata Shirin Amurka Ne Don Matsa lamba Kan Kasashen Iran Da Rasha                                                                                                                                                                     
  • An gano gawar mutum 15 bayan hatsarin kwalekwale a Neja
  • An gano gwawar mutum 15 bayan hatsarin kwalekwale a Neja