Tsofaffin Ma’aikatan FRCN Za Su Gudanar da Zanga-zanga Kan Jinkirin Biyan Hakkokin Su
Published: 8th, April 2025 GMT
Kungiyar Tsofaffin Ma’aikatan Hukumar Gidan Rediyon Tarayya (FRCN) ta Umarci Mambobinta a Fadin Kasa da Su Gudanar da Zanga-zanga Kan Jinkirin Biyan Kudin Fansa da Aka Yi Alkawari Tsawon Shekaru.
A cikin wata sanarwa, kungiyar ta bayyana cewa zanga-zangar da aka shirya gudanarwa a ranar Laraba na da nufin jawo hankalin hukumomi masu ruwa da tsaki kan kalubalen da tsofaffin ma’aikata ke fuskanta.
Ana sa ran zanga-zangar za ta fara ne a hedikwatar Gidan Rediyon Najeriya da ke Abuja da misalin karfe goma na safe, sannan ta ci gaba zuwa wasu wurare cikin lumana, yayin da masu shirya zanga-zangar suka bukaci a tabbatar da cikakken daukar rahoton al’amarin daga kafafen yada labarai.
Jagororin zanga-zangar sun nuna rashin jin dadinsu kan zargin gaza biyan kudaden fansa daga Hukumar Tsare-tsaren Biyan Fansho (PTAD), duk da cewa an ce an amince da biliyoyin naira domin biyan su.
Wasu daga cikin tsofaffin ma’aikatan da suka nuna goyon baya ga zanga-zangar sun bayyana mamaki kan irin shiru da kungiyar FRCN na kasa ke yi game da wannan batu mai matukar muhimmanci, wanda bai kamata a ci gaba da dauka da wasa ba, musamman ganin halin kuncin da masu ritaya ke ciki.
Suleiman Kaura
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: zanga zangar
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Ci gaba da killace Gaza da kuma kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, laifi ne da ba a taba yin irinsa ba a tarihin dan Adam
A wata tattaunawa ta wayar tarho da takwaransa na Masar Badar Abdel Ati a yammacin jiya Lahadin da ta gabata, Araqchi ya bayyana ci gaba da killace yankin Gaza da rashin abinci da magunguna, tare da kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, a matsayin wani laifi da ba a taba ganin irinsa ba a tarihin dan Adam. Ya dauki Amurka da sauran masu goyon bayan ‘yan sahayoniyya a matsayin masu hannu a kisan kiyashi da laifukan yaki da ake aikatawa a Gaza.
Ministan harkokin wajen na Iran ya jaddada wajibcin tunkarar muggan manufofin yahudawan sahayoniyya na tilastawa al’ummar Gaza da yammacin kogin Jordan yin hijira daga muhallinsu, yana mai bayyana halin ko in kula da kasashen duniya suke nun awa kan wadannan laifuka a matsayin abin mamaki da damuwa.
Araghchi ya kuma yi wa takwaransa na Masar bayani kan ci gaban tattaunawar Iran da Amurka kan Shirin makamashin nukiliya na zaman lafiya da ake takaddama a kai tsawon shekaru.