Tsofaffin Ma’aikatan FRCN Za Su Gudanar da Zanga-zanga Kan Jinkirin Biyan Hakkokin Su
Published: 8th, April 2025 GMT
Kungiyar Tsofaffin Ma’aikatan Hukumar Gidan Rediyon Tarayya (FRCN) ta Umarci Mambobinta a Fadin Kasa da Su Gudanar da Zanga-zanga Kan Jinkirin Biyan Kudin Fansa da Aka Yi Alkawari Tsawon Shekaru.
A cikin wata sanarwa, kungiyar ta bayyana cewa zanga-zangar da aka shirya gudanarwa a ranar Laraba na da nufin jawo hankalin hukumomi masu ruwa da tsaki kan kalubalen da tsofaffin ma’aikata ke fuskanta.
Ana sa ran zanga-zangar za ta fara ne a hedikwatar Gidan Rediyon Najeriya da ke Abuja da misalin karfe goma na safe, sannan ta ci gaba zuwa wasu wurare cikin lumana, yayin da masu shirya zanga-zangar suka bukaci a tabbatar da cikakken daukar rahoton al’amarin daga kafafen yada labarai.
Jagororin zanga-zangar sun nuna rashin jin dadinsu kan zargin gaza biyan kudaden fansa daga Hukumar Tsare-tsaren Biyan Fansho (PTAD), duk da cewa an ce an amince da biliyoyin naira domin biyan su.
Wasu daga cikin tsofaffin ma’aikatan da suka nuna goyon baya ga zanga-zangar sun bayyana mamaki kan irin shiru da kungiyar FRCN na kasa ke yi game da wannan batu mai matukar muhimmanci, wanda bai kamata a ci gaba da dauka da wasa ba, musamman ganin halin kuncin da masu ritaya ke ciki.
Suleiman Kaura
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: zanga zangar
এছাড়াও পড়ুন:
Miliyoyin Mutane Sun Gudanar Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
A yau Asabar aka gudanar da bikin ranar ” Idin Gadir” a nan birnin Tehran, wanda ya tashi daga dandalin “Inqilab” zuwa dandalin ” Azadi” mai nisan kilo mita 10. Bisa la’akari da halin yake da ake ciki, an bai wa bikin na bana taken: Iran ce, takobin Zulfikar Na Imam Ali.”
Miliyoyin mutane ne dai su ka cika filin bikin na birnin Tehran da mutane su ka fara taruwa tun da tsakar rana, har zuwa bayan faduwar rana. A bisa kirdado kusan mutane miliyan 3 ne su ka taru a nan Tehran.
A cikin sauran birane da garuruwan Iran an yi wannan irin gangamin na raya ranar Idin Gadir wanda yake tattare da girmama shahidan da su ka kwanta dama sanadiyyar hare-haren ta’addancin HKI. Haka nan kuma mahalarta bikin na Gadir sun jinjinawa dakarun kare juyin musulunci na Iran da kuma sojojin kasar akan martanin da su ka mayarwa da HKI a daren jiya Juma’a da kuma a yau Asabar.