Rahoto: Yara Falasdinawa 350 ne Isra’ila ke tsare da su a gidajen kurkuku
Published: 7th, April 2025 GMT
A cewar cibiyar yada labaran Falasdinu, a yayin bikin ranar yara kanana ta duniya a Falasdinu, cibiyoyi masu fafutuka kan harkokin fursunoni sun sanar da cewa: Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila tana ci gaba da tsare kananan yara Palastinawa sama da 350 a gidajen yari da wuraren da ake tsare da fursunoni.
Sanarwar hadin gwiwa da hukumar kula da harkokin tsare-tsare, da “Kungiyar Fursunonin palasdinu”, da kuma “Cibiyar Kare Hakkokin Bil Adama ta Al-Dameer” suka fitar, ta bayyana cewa, yaran na fuskantar matsaloli Ciki har da azabtarwa, yunwa da gangan, da rashin kulawar likita.
Wadannan cibiyoyi sun jaddada cewa yaran Palasdinawa su ma suna fuskantar tauye hakkinsu, wanda irin wannan hali ne ya yi sanadin shahadar wani yaro a cikin makon nan a gidan yarin Isra’ila.
A cewar wadannan kungiyoyi, tsare yara bias irin wannan tsari na Isra’ila yana karuwa, kuma manufarsu ita ce kawar da yaran daga cikin iyalansu da lalata kuruciyarsu. Kuma wannan shi ne a lokacin da aka fi kai hare-hare mafi muni a tarihi kan yaran Palastinawa, yayin da ake ci gaba da kisan kiyashin, dubban yara ne suka yi shahada, wasu dubbai kuma suka jikkata ko kuma sun rasa iyalansu.
Kungiyoyin kare hakkin bil adama sun kuma sanar da cewa, tun bayan da aka fara kisan kiyashin, an samu sauye-sauye a halin da ake ciki na fursunoni yara.
Game da yara a Gaza, saboda ci gaba da tilsta manufar korar jama’a daga yankunansu da Isra’ila ke aiwatarwa, yara da dama sun rabu da iyalansu.
Duk da tsauraran matakan hana kai ziyara, kungiyoyin lauyoyi sun yi nasarar ganawa da wasu daga cikin yaran da ake tsare da su a gidajen yarin Ofer, Megiddo, da Damon, kuma an tattara shedu da dama da suka nuna irin yadda ake azabtar da su da kuma tauye hakki akan wadannan yaran.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
Babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin CMG, ya gabatar da labarin ganawar da aka yi jiya Alhamis tsakanin shugabannin Sin da Amurka a Busan na Korea ta Kudu, cikin harsuna 85. Kuma zuwa yau Juma’a, mutanen da suka karanta rahotanni masu alaka da ganawar ta hanyoyin watsa labarai na dandalin CMG sun kai miliyan 712. Haka kuma, kafafen watsa labarai na kasa da kasa 1678, sun wallafa tare da tura rahotanni da bidiyon labaran CMG na harsuna daban daban game da ganawar, har sau 4431.
Har ila yau a wannan rana, an gudanar taron tattaunawa na kasa da kasa kan bude kofa da kirkire kirkire da ci gaba na bai daya a kasar Uruguay, wanda CMG da hadin gwiwar ofishin jakadancin Sin dake kasar suka shirya a Montevideo babban birnin Uruguay. (Mai fassara: FMM)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA