HausaTv:
2025-11-03@03:02:56 GMT

Rahoto: Yara Falasdinawa 350 ne Isra’ila ke tsare da su a gidajen kurkuku

Published: 7th, April 2025 GMT

A cewar cibiyar yada labaran Falasdinu, a yayin bikin ranar yara kanana ta duniya a Falasdinu, cibiyoyi masu fafutuka kan harkokin fursunoni sun sanar da cewa: Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila tana ci gaba da tsare kananan yara Palastinawa sama da 350 a gidajen yari da wuraren da ake tsare da fursunoni.

Sanarwar hadin gwiwa da hukumar kula da harkokin tsare-tsare, da “Kungiyar Fursunonin palasdinu”, da kuma “Cibiyar Kare Hakkokin Bil Adama ta Al-Dameer” suka fitar, ta bayyana cewa, yaran na fuskantar matsaloli Ciki har da azabtarwa, yunwa da gangan, da rashin kulawar likita.

Wadannan cibiyoyi sun jaddada cewa yaran Palasdinawa su ma suna fuskantar tauye hakkinsu, wanda irin wannan hali ne ya yi sanadin shahadar wani yaro a cikin makon nan a gidan yarin Isra’ila.

A cewar wadannan kungiyoyi, tsare yara bias irin wannan tsari na Isra’ila yana karuwa, kuma manufarsu ita ce kawar da yaran daga cikin iyalansu da lalata kuruciyarsu. Kuma wannan shi ne a lokacin da aka fi kai hare-hare mafi muni a tarihi kan yaran Palastinawa, yayin da ake ci gaba da kisan kiyashin, dubban yara ne suka yi shahada, wasu dubbai kuma suka jikkata ko kuma sun rasa iyalansu.

Kungiyoyin kare hakkin bil adama sun kuma sanar da cewa, tun bayan da aka fara kisan kiyashin, an samu sauye-sauye a halin da ake ciki na fursunoni yara.

Game da yara a Gaza, saboda ci gaba da tilsta manufar korar jama’a daga yankunansu da Isra’ila ke aiwatarwa, yara da dama sun rabu da iyalansu.

Duk da tsauraran matakan hana kai ziyara, kungiyoyin lauyoyi sun yi nasarar ganawa da wasu daga cikin yaran da ake tsare da su a gidajen yarin Ofer, Megiddo, da Damon, kuma an tattara shedu da dama da suka nuna irin yadda ake azabtar da su da kuma tauye hakki akan wadannan yaran.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

Babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin CMG, ya gabatar da labarin ganawar da aka yi jiya Alhamis tsakanin shugabannin Sin da Amurka a Busan na Korea ta Kudu, cikin harsuna 85. Kuma zuwa yau Juma’a, mutanen da suka karanta rahotanni masu alaka da ganawar ta hanyoyin watsa labarai na dandalin CMG sun kai miliyan 712. Haka kuma, kafafen watsa labarai na kasa da kasa 1678, sun wallafa tare da tura rahotanni da bidiyon labaran CMG na harsuna daban daban game da ganawar, har sau 4431.

 

Har ila yau a wannan rana, an gudanar taron tattaunawa na kasa da kasa kan bude kofa da kirkire kirkire da ci gaba na bai daya a kasar Uruguay, wanda CMG da hadin gwiwar ofishin jakadancin Sin dake kasar suka shirya a Montevideo babban birnin Uruguay. (Mai fassara: FMM)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
  • Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar
  • Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Duk Wani Kutse Na Isra’ila A Kudancin Kasar