Aminiya:
2025-06-15@00:02:07 GMT

’Yan sanda sun janye gayyatar da suka yi wa Sanusi II kan hawan sallah

Published: 7th, April 2025 GMT

Sufeto Janar na ’Yan Sandan Najeriya, Kayode Egbetokun, ya janye gayyatar da aka yi wa Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, kan hawan sallah.

Maimaikon ya Sarkin ya je Abuja domin yi masa tambayoyi, Sufeto Janar ya umarci rundunar ’yan sandan jihar, yi wa Sanusi II tambayoyi.

Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da hare-haren Filato, sun nemi a yi adalci Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Taraba

Kakakin ’yan sanda na ƙasa, Olumuyiwa Adejobi ne, ya bayyana hakan, inda ya ce an soke gayyatar ne bayan da wasu manyan mutane a ƙasar suka shiga lamarin.

Ya ƙara da cewa ’yan sanda na son kauce wa duk wani da zai danganta lamarin da siyasa ko wani abu daban.

Idan ba a manta ba hedikwatar ’yan sanda ta ƙasa ce, ta gayyaci Sarkin, domin ya bayar da bayani game da wani abin da ya faru a lokacin bikin Sallah a Kano.

Tun da farko, rundunar ’yan sandan jihar, ta dakatar da duk wasu hawan Sallah da suka haɗa da jerin gwanon dawakai, saboda matsalar tsaro.

Amma a ranar 30 ga watan Maris, yayin da Sarkin ke tafiya zuwa filin Idi na Ƙofar Mata domin Sallar Idi, an kashe wani jami’in sa-kai da ke tsaronsa ta hanyar caka masa wuƙa, sannan wasu kuma sun jikkata.

Bayan haka, wasu majiya sun ce Sufeto Janar na ’yan sanda, Kayode Egbetokun, ne, ya umarci Kwamishinan ’yan sandan jihar da ya kama Sanusi II.

Sai dai Kwamishinan ya shaida masa cewa abin da ya faru bai shafi karya dokar hana hawan Sallah ba, kuma Sarkin bai hau doki ba wajen ziyarar gidan gwamnati kamar yadda ake yi a da.

Sai dai duk haka Sufeton ya umarci sashen leƙen asiri na ’yan sanda da su gayyaci Sarkin zuwa Abuja domin amsa tambayoyi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hawan Sallah Sufeto Janar Na Yan Sanda Tambayoyi

এছাড়াও পড়ুন:

Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35

Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta zama kasa ta farko a duniya da ta harbo jiragen saman yaki kirar F-35

Iran ta zama kasa ta farko a duniya da ta yi nasarar harbo jiragen yaki kirar F-35, bayan da ta yi nasarar auna wasu jiragen saman yakin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila kirar F-35 guda biyu, kuma ta barar da su kasa.

Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta yi amfani da wadannan jirage masu tsananin ci gaban zamani wajen kai hare-haren wuce gona gona da iri kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran da safiyar ranar Juma’a, wanda hare-haren suka yi sanadiyyar shahadar wasu manyan jami’an sojan Iran da masana kimiyyar nukiliya da fararen hula da suka hada da mata da kananan yara.

Ma’aikatar hulda da jama’a ta rundunar sojojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta sanar a cikin wata sanarwa da ta fitar cewa: Dakarun tsaron saman Iran sun harbo jiragen saman yaki kirar F-35 guda biyu, baya ga wasu jiragen saman yakin yahudawan sahayoniyya marasa matuka ciki.

Sanarwar ta nuna cewa: Jami’an tsaron Iran sun kame daya daga cikin matukan jiragen wacce mace ce, kuma ana kan bincike domin sanin makomar matukin daya jirgin.

Abin lura shi ne cewa: Jiragen yakin kirar F-35 da ‘yan sahayoniyya ke amfani da su na daga cikin wadanda suka ci gaba a duniya kuma ake gwada su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Gobara Ta Ƙone Wani Gidan Mai A Legas
  • Zan Ci Gaba Da Ɓata Wa Masu Sukar Tinubu Rai Da Ayyuka – Wike