Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar, ya bayyana rashin jin daɗinsa dangane da kashe matafiya ’yan Arewa da aka yi a Jihar Edo.

Saboda haka Sarkin ya ce suna dakon ganin hukuncin da za a ɗauka dangane da faruwar wannan mummunan lamari.

Kisan Mafarauta: Matakan da gwamnatin Edo da ta Kano suke ɗauka Dalilin da muka soke Hawan Bariki — Masarautar Zazzau

Da yake miƙa saƙon gaisuwar Sallah ga Gwamnan Sakkwato, Alhaji Ahmad Aliyu a ranar Litinin, Sarkin ya ce “mun ga an ɗauki mataki kan yanayin da ake ciki a Jihar Edo.

“Saboda haka muna jiran ganin hukuncin da za a ɗauka bayan kammala bincike don ba wani dalili ka kashe mutum ba tare da wani haƙƙi ba.

“Muna kiran jami’an tsaro da su tashi tsaye domin tabbatar da cewa jama’a ba su fusata ba sun ɗauki hukunci a hannunsu.

“Idan a wani wurin mutanen banza sun ɗauki hukunci a hannunsu, mu a nan Sakkwato ba za mu bari a yi abin da bai kamata ba.

“Mu sanya ’yan uwanmu da abin ya faru da su a cikin addu’a sannan muna kiran gwamnati da jami’an tsaro su ɗauki matakin kare rayukkan jama’a,” a cewar Sarkin Musulmi.

Sarkin ya ƙara da cewa “bai kamata a riƙa yaɗa abin da bai dace ba a kafafen sadarwa na zamani da za su janyo tashin hankali a wurin da ake da zaman lafiya.

“Duk wani abu da ya faru a wani wuri, bai kamata wasu da ke can wani wurin na daban su ce za su ɗauki mataki a Sakkwato ko Kano ko Kaduna kan wani abun da ya faru a Jihar Edo ko Legas ba.”

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano mafarauta Yan Arewa

এছাড়াও পড়ুন:

Yarima Mai Jiran Gadon Saudiyya Ya Jaddada Goyon Bayan Kasarsa Ga Iran

Yarima mai jiran gadon Saudiyya ya tabbatarwa shugaban kasar Iran cewa: Saudiyya tana goyon bayan Iran

Yariman mai jiran gadon Saudiyya Mohammed bin Salman ya tabbatar da hakan ne a wata tattaunawa ta wayar tarho da shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian a yammacin jiya Asabar, yana mai jaddada cewa: Masarautar Saudiyya da daukacin al’ummar musulmin duniya sun hadu a kan goyon bayan Iran.

Yarima mai jiran gadon sarautar Saudiyya ya ce: Dukkanin al’ummomin kasashen musulmi a yau suna da hadin kai da jaddada goyon bayansu ga Iran, kuma yana iyaka kokarinsa a fagen diflomasiyya da matsin lamba na kasa da kasa don dakatar da wuce gona da irin da ‘yan sahayoniyya suke yi kan Iran.

Bin Salman ya yi Allah wadai da hare-haren rashin adalci da ‘yan sahayoniyya suke kaiwa Iran.

Ya kuma bayyana jimaminsa tare da jajantawa al’ummar kasar Iran dangane da wadannan hare-hare da suka rutsa da su, yana mai jaddada cewa: Saudiyya tana da tabbataccen matsayi kan tsayawa tare da ‘yar uwarta Jamhuriyar Musulunci ta Iran, kuma duniyar musulmi a yau ta hade kan muryar daya wajen goyon bayan Iran.

Ya ci gaba da cewa: “Mun yi imanin cewa, gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila na neman ta hanyar kara kunna wutar rikici ta janyo Amurka a cikin tsakiyar rikici, amma suna da yakinin cewa martanin Iran a kan ma’aunin daidaito da matakan hankali zai dakile wannan  yunƙurin makirci.”

Bin Salman ya kuma jaddada cewa: Kasarsa ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen bayar da duk wani tallafi da ya dace ga ‘yan uwanta Iran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa
  • Yarima Mai Jiran Gadon Saudiyya Ya Jaddada Goyon Bayan Kasarsa Ga Iran
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Darussan Hadisin Aikin Hajjin Manzon Allah S.A.W (2)
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara