Kwankwaso Ya Yi Allah-wadai Da Kisan ‘Yan Arewa A Edo, Ya Buƙaci A Yi Adalci
Published: 28th, March 2025 GMT
Kwankwaso ya buƙaci hukumomin da abin ya shafa da su gudanar da cikakken bincike tare da tabbatar da cewa an hukunta masu laifin.
“Ina kira ga hukumomin da abin ya shafa da su gudanar da cikakken bincike a kan wannan lamari mai tayar da hankali tare da tabbatar da an hukunta masu hannu a ciki,” in ji shi.
Tsohon gwamnan ya kuma miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan mamatan, da gwamnatin Kano da sauran jihohin da abin ya shafa, tare da yin addu’ar Allah Ya jiƙansu.
Kisan ya haifar da cece-ku-ce kan hatsarin da ke tattare da ɗaukar doka a hannu, tare da buƙatar a ƙara inganta tsaro don hana irin haka faruwa a gaba.
Jagororin siyasa da na al’umma da dama sun goyi bayan kiran da Kwankwaso ya yi na neman adalci, tare da buƙatar gwamnati ta ɗauki matakin gaggawa a kan waɗanda suka aikata wannan ta’asa.
Yayin da bincike ke ci gaba, ana ci gaba da matsin lamba kan hukumomin tsaro don tabbatar da cewa an yi adalci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Yan Arewa Kwankwaso
এছাড়াও পড়ুন:
Sakon Jagora : Isra’ila ta jira hukunci mai tsanani bayan hari kan Iran
Bayan harin da gwamnatin Sahayoniya ta kai kasarmu, Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya aike da sako ga al’ummar Iran. Ga sakon kamar haka
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai
Al’ummar Iran masu daraja!
Gwamnatin yahudawan sahyoniya ta hanyar aikata wani laifi da sanyin safiyar yau, ta sake bayyana munanan dabi’arta da fasadi.
Ta hanyar kai hari dole ne wannan ya fuskanci hukunci mai tsanani.
A wannan harin makiya, kwamandoji da masana kimiyya da dama sun yi shahada.
Wadanda suka gaje su kuma da abokan aikinsu za su ci gaba da aiki nan take akan wannan tafarki, godiya ta tabbata ga Allah.
Ta hanyar wannan danyen aiki, gwamnatin Sahayoniya ta kaddara akan ta cewa zata fuskanci martini mai radadi.