Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa gwamnatin kasar ta Mayarwa Shugaban kasar Amurka Donal Trump amsar wasikarsa ga kasar danagne da shirinta na makashain Nulkiya ta hanyar kasar Omman.

Aragchi ya bayyana haka a jiya Alhamis a lokacinda yake hira da kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran.

Ya kuma kara da cewa a cikin wasikar dai gwamnatin JMI bayyanawa shugaban kan cewa tana ganin bazata iya shiga tattaunawa gaba da gaba da Jami’an gwamnatin kasar Amurka dangane da shirinta na makamashin Nukliya ba, saboda halayen gwamnatocin Amurka a baya dangane da shirin.

Daga ciki Iran ta dauke shekaru biyu cutar tana tattauna batun wannan shirin da manya-manyan kasashen duniya daga ciki har da kasar Amurka,  aka cimma yarjeniya a shekara ta 2015, kuma har an fara aiwatar da yarjeniyar ta JCPOA, amma gwamnatin Amurka ta lokacinda wanda shugaba mai ci yake jagoranta ta fice daga cikin yarjeniyar ba tare da wani dalili ba, sannan ta dorawa Iran sabbin takunkuman tattalin arziki mafi muni a tarihin kasar da nufin tilasta mata da sake wata tattaunawa  da ita. Waya ya sani mai yuwa da sake saba alkawalin da aka cimma da ita a wannan karon ma, bayan wancan?. Amma ta kasa samun nasara har ta sauka.

Banda haka a lokacinda wannan gwamnatin ta zo kan karagar shugabancin Amurka ta fara kara dorawa JMI wasu karin takunkuman tattalin arziki kafin ma ta gayyana kasar zuwa tattaunawa.

Wannan ya nuna cewa ba tattaunawa take bukata ba, sai dai tursasawa. Wanda kasar Iran baza ta taba amincewa da haka ba.

Sannan idan Amurka ta na son shiga tattaunawa da Iran kan shirinta na makamashin Nukliya to a halin yanzu ma tana tattaunawa da kasashen turai uku kan shirin nata. Sai ta shigo.

 

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Amurka

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin

Yayin taron shekara-shekara na tattaunawar CBD na shekarar 2025 da aka rufe a yau Juma’a 13 ga wata, mashawarci kana kwararre a hukumar kasuwancin kasar Sin ta kasar Birtaniya, kuma shugaban cibiyar bunkasa kasuwanci tsakanin Birtaniya da Sin mista John Mclean, ya bayyana yayin da yake hira da wakilin CMG cewa, kasuwar kasar Sin tana cike da damammaki, don haka dole ne ya shiga a dama da shi a cikinta. A ganinsa, yayin da ake tinkarar tashe-tashen hankula da rashin tabbaci a duniya, babbar baiwar da Sin take da ita, da muhalli mai aminci da bude kofa ga kowa, sun samarwa kamfanonin Birtaniya da ma duniya baki daya damammaki.

Tun bayan kafuwarsa a shekarar 2000 zuwa yanzu, taron ya kasance dandali da kasar Sin ke tattaunawa da kasashen duniya. A yayin taron bana, wakilai fiye da 6000 daga sassan siyasa, da kasuwanci, da ilimi da suka fito daga kasashe da yankuna fiye da 40 sun halarta. A lokacin gudanar da taron, wasu mahalartansa sun yi nuni da cewa, kasar Sin na da babbar juriya wajen raya tattalin arziki, da kuma babbar baiwar raya kasa. Haka kuma, gwamnatin Sin ta gaggauta raya sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko, lamarin da ya zuba sabon kuzari ga kamfanonin kasashen waje, ta yadda suke shiga a dama da su wajen yin ciniki a kasar Sin.

A yayin bikin bude taron, mahalartansa sun yi kira da a gina duniya mai tsabta, da kyawu, da dorewa cikin hadin gwiwa, duba da ganin kasar Sin ta ba da babbar gudummawa, ta kuma yi iyakacin kokari a fannin raya kasa ba tare da gurbata muhalli ba, da kuma rage fitar da sinadarin carbon. Alkaluma sun nuna cewa, yanzu haka kasar Sin tana daya daga cikin kasashen da suka fi saurin rage yawan makamashi mai dumama yanayi da suke amfani da shi da samun kyautatuwar iska, ta kuma dasa yawan bishiyoyi, da ciyayi da fadinsu ya kai rubu’i bisa jimillar fadin sabbin bishiyoyi da ciyayi na duniya baki daya, tare da kafa tsarin makamashin da ake sake amfani da shi mafi girma, kuma mafi saurin ci gaba a duniya, baya ga kafa tsarin masana’antu na sabbin makamashi mafi girma kuma cikakke a duniya. (Tasallah Yuan)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
  • Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya
  • Iran ta Yi Gargadin Cewa Zata Fice Daga Yarjeniyar NPT Idan Hukumar IAEA Ta Tir Da Ita
  • Ministan Tsaro Na Kasar Iran ya bada Labarin Gwajin Wani Sabom Makami Mai Limzami Mai Daukar abubuwan Fashewa Har Ton Biyu
  • Ministan man Fetur na Kasar Iran Yace Amurka Ta Kasa Hana Iran Saida Danyen Man Fetur Na Kasar