Leadership News Hausa:
2025-09-18@08:23:39 GMT

Mutane Miliyan 9 Na Iya Kamuwa Da Cutar HIV Saboda Rashin Tallafi

Published: 25th, March 2025 GMT

Mutane Miliyan 9 Na Iya Kamuwa Da Cutar HIV Saboda Rashin Tallafi

Sai dai duk da yaba wa Amurka bisa irin taimakon da ta bayar a baya, Byanyima ta nuna damuwa kan yadda aka dakatar da tallafin kwatsam ba tare da shiri ba.

Wannan na iya haddasa koma baya a ƙoƙarin da aka shafe shekaru ana yi na rage yawan masu kamuwa da cutar, musamman a yankunan da ke fama da talauci da ƙarancin kayan kiwon lafiya.

Masana kiwon lafiya sun bayyana cewa, idan ba a samu sabbin hanyoyin tallafi ba, yiwuwar ƙaruwar mace-mace sakamakon cutar HIV na da matuƙar girma.

Hakan na iya rusa nasarorin da aka samu a yaƙin da duniya ke yi da cutar.

Ana ci gaba da kira ga ƙasashen duniya da ƙungiyoyin agaji da su ceto shirin da ke kare miliyoyin rayuka daga barazanar cutar HIV.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Majalisar Dinkin Duniya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Zamfara Ta Nemi Karin Tallafi Ga ‘Yan Gudun Hijira

Gwamnatin Jihar Zamfara ta roki Hukumar Raya Kasashen Waje ta Kasa (FCDO), Premier Urgence Internationale (PUI), da sauran masu ruwa da tsaki da su kara tallafa wa ‘yan gudun hijirar da ke jihar.

 

Kwamishinan Bada Agaji na Jiha Alhaji Salisu Musa Tsafe ne ya yi wannan kiran a lokacin da yake jawabi ga mahalarta taron na kwana guda kan shirin ceton rayuka da karfafawa da kuma juriya (LEARP) wanda kungiyar FCDO ta dauki nauyin shiryawa a Abuja.

 

A wata sanarwa dauke da sa hannun Daraktan Yada Labarai na Ma’aikatar, Bashir Kabiru Ahmad, Kwamishinan ya bayyana cewa a halin yanzu jihar na karbar dubban ‘yan gudun hijira daga al’ummomi sama da 1,008 a fadin kananan hukumomin 14, kamar yadda aka gani a cikin rajistar zamantakewa na jihar.

 

Alhaji Musa Tsafe ya bayyana cewa, tallafin da ake bukata ya hada da bangarorin Rayuwa, Karfafawa, samun tallafin Kudi da Manufofi da sauran abubuwan da za a iya yi da nufin rage radadin halin da ‘yan gudun hijira  ke ciki a jihar.

 

Alhaji Tsafe ya yabawa abokan aikin raya kasa bisa yadda suke ci gaba da tallafawa ‘yan gudun hijira da sauran marasa galihu a Zamfara.

 

A cewarsa, aikin da aka tsara domin aiwatar da shi da kungiyar Premier Urgence International (PUI) za ta yi zai kasance muhimmin taimako ga al’ummar jihar Zamfara.

 

Ya bayyana taron a matsayin wani ci gaba a kokarin jihar na inganta rayuwar ‘yan gudun hijira da marasa galihu musamman mata da yara.

 

 

Alhaji Tsafe ya tabbatarwa da abokan huldar cewa jihar Zamfara karkashin Gwamna Dauda Lawal ta samar da tsarin siyasa da samar da yanayin da kungiyoyin agaji ke gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

 

REL/AMINU DALHATU.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fasahar AI ta gano cutar da za ta kama mutane a shekara 10 masu zuwa
  • Gwamnatin Zamfara Ta Nemi Karin Tallafi Ga ‘Yan Gudun Hijira
  • Uwargidan Shugaban Kasa, Oluremi Tinubu Ta Yi Kira Ga Zaman Lafiya A Duniya
  • ’Yan bindiga sun sako ma’auratan da suka sace a Katsina bayan biyan N50m
  • UNICEF Ya Ba Da Tallafin Kayayyakin Aiki Ga Cibiyoyin Lafiya A Kirikasamma
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
  • KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta