Mutane Miliyan 9 Na Iya Kamuwa Da Cutar HIV Saboda Rashin Tallafi
Published: 25th, March 2025 GMT
Sai dai duk da yaba wa Amurka bisa irin taimakon da ta bayar a baya, Byanyima ta nuna damuwa kan yadda aka dakatar da tallafin kwatsam ba tare da shiri ba.
Wannan na iya haddasa koma baya a ƙoƙarin da aka shafe shekaru ana yi na rage yawan masu kamuwa da cutar, musamman a yankunan da ke fama da talauci da ƙarancin kayan kiwon lafiya.
Masana kiwon lafiya sun bayyana cewa, idan ba a samu sabbin hanyoyin tallafi ba, yiwuwar ƙaruwar mace-mace sakamakon cutar HIV na da matuƙar girma.
Hakan na iya rusa nasarorin da aka samu a yaƙin da duniya ke yi da cutar.
Ana ci gaba da kira ga ƙasashen duniya da ƙungiyoyin agaji da su ceto shirin da ke kare miliyoyin rayuka daga barazanar cutar HIV.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Majalisar Dinkin Duniya
এছাড়াও পড়ুন:
Ruwa Kamar Da Bakin Kwarya Ya Ci Rayukan Mutane 25 A Jihar Rivers
Mamakon ruwan sama da ya sauka a jihar Rivers ta Najeriya ya yi gyara, tare da daukar rayukan mutane 25,kamar yadda hukumar agajin gaggawa ta kasar ta sanar.
Ruwan da ya sauka a garin Okrika ya haddasa zaizayar kasa,wacce ta binne gidaje da dama, da kuma yin awon gaba da mutane.
Masu ayyukan ceto sun ce har yanzu ana ci gaba da gano gawawwakin mutane a karkashin baraguzai. Haka nan kuma mutane da dama sun rasa matsugunansu.
Duk da cewa ana ci gaba da ayyukan ceto said ai har yanzu da akwai yankuna da ba za a iya shiga cikinsu ba saboda sun yi lungu.