Leadership News Hausa:
2025-06-01@00:20:14 GMT

Mutane Miliyan 9 Na Iya Kamuwa Da Cutar HIV Saboda Rashin Tallafi

Published: 25th, March 2025 GMT

Mutane Miliyan 9 Na Iya Kamuwa Da Cutar HIV Saboda Rashin Tallafi

Sai dai duk da yaba wa Amurka bisa irin taimakon da ta bayar a baya, Byanyima ta nuna damuwa kan yadda aka dakatar da tallafin kwatsam ba tare da shiri ba.

Wannan na iya haddasa koma baya a ƙoƙarin da aka shafe shekaru ana yi na rage yawan masu kamuwa da cutar, musamman a yankunan da ke fama da talauci da ƙarancin kayan kiwon lafiya.

Masana kiwon lafiya sun bayyana cewa, idan ba a samu sabbin hanyoyin tallafi ba, yiwuwar ƙaruwar mace-mace sakamakon cutar HIV na da matuƙar girma.

Hakan na iya rusa nasarorin da aka samu a yaƙin da duniya ke yi da cutar.

Ana ci gaba da kira ga ƙasashen duniya da ƙungiyoyin agaji da su ceto shirin da ke kare miliyoyin rayuka daga barazanar cutar HIV.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Majalisar Dinkin Duniya

এছাড়াও পড়ুন:

Ruwa Kamar Da Bakin Kwarya Ya Ci Rayukan Mutane 25 A Jihar Rivers

 Mamakon ruwan sama da ya sauka a jihar Rivers ta Najeriya ya yi gyara, tare da daukar rayukan mutane 25,kamar yadda hukumar agajin gaggawa ta kasar ta sanar.

Ruwan da ya sauka a garin Okrika ya haddasa zaizayar kasa,wacce ta binne gidaje da dama, da kuma yin awon gaba da mutane.

Masu ayyukan ceto sun ce har yanzu ana ci gaba da gano gawawwakin mutane a karkashin baraguzai. Haka nan kuma mutane da dama sun rasa matsugunansu.

Duk da cewa ana ci gaba da ayyukan ceto said ai har yanzu da akwai yankuna da ba za a iya shiga cikinsu ba saboda sun yi lungu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa
  • Likitocin Iran Suna Ci Gaba Da Samun Nasara Wajen Magance Matsalar Kurmanta Da Na Bebantaka
  • Cutar Kwalara Ta Yadu A Sudan Baya Ga Matsalar Tashe-Tashen Hankulan Da Suke Ci Gaba Da Yuduwa A Kasar
  • Hana shigar da abinci da Isra’ila ta yi zuwa Gaza ‘laifi ne na yaki’: MDD
  • Ruwa Kamar Da Bakin Kwarya Ya Ci Rayukan Mutane 25 A Jihar Rivers
  • Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar
  • Zazzaɓin Lassa da sanƙarau ya kashe mutum 366 a jihohi 24 – NCDC
  • Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke
  • MDD Ta Gudanar Da Bikin Ranar Tunawa Da Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Duniya Ta 2025
  • Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Ayukka 16 A Sakkwato