Aminiya:
2025-11-03@07:44:04 GMT

Mutum 2,000 za su riƙa kamuwa da cutar HIV duk rana a duniya — MDD

Published: 25th, March 2025 GMT

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin cewa za a samu mutum 2,000 sabbin kamuwa da cutar SIDA duk rana a faɗin duniya.

MDD ta ce tana wannan gargaɗi ne sakamakon matakin Amurka na katse taimakon agajin ƙasashen duniya ƙarƙashin Hukumar ta USAID.

Matasa sun daka wawa kan kayan abincin da Seyi Tinubu zai raba a Gombe Gwamnonin PDP sun garzaya Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas

MDD ta ce ce tilas ne a maye gurbin taimakon idan ana neman kare duniya daga shiga annobar cutar ta AIDS.

.

Hukumar ta ce muddun Amurka ba ta dawo da tallafin daƙile cutar ba, kuma ba a samu maye gurbin taimakon na Amurka ba, nan da shekaru huɗu za a samu kimanin mutane miliyan 6.3 sabbin masu kamuwa da cutar ta AIDS ko SIDA, gami da samun ƙarin masu mutuwa daga cutar.

Da take jawabi a Geneva a ranar Litinin, Winnie Byinyama, ta ce za a samu sabbin masu kamuwa da cutar aƙalla guda 2,000 kullum saboda janye tallafin, tana mai cewa tuni dubban likitoci da sauran ma’aikatan jinya sun fara rasa aikinsu.

Sai dai duk da haka ta yaba da gudunmawar Amurka wajen tallafa wa ayyukan kiwon lafiya a duniya a gomman shekaru da suka gabata.

Amma ta ce yadda kwatsam aka dakatar da tallafin ba tare da shiri ba, ya fara kawo tsaiko a ƙoƙarin da ake yi na yaƙi da cutar ta HIV.

Alƙaluman da aka fitar a shekarar 2023 sun nuna cewa kimanin mutum 600,000 suka rasa rayukansu a faɗin duniya sakamakon Cutar ta SIDA.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: kamuwa da cutar

এছাড়াও পড়ুন:

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba November 2, 2025 Manyan Labarai 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su November 2, 2025 Manyan Labarai Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali
  • Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba
  • Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
  • Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
  • Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi