HausaTv:
2025-06-15@18:26:29 GMT

Dakarun Yemen sun kara kai hare-hare goyan bayan Falasdinu

Published: 25th, March 2025 GMT

Dakarun sojin Yaman sun ce sun kara kai hare-hare na nuna kyama ga Isra’ila da Amurka a matsayin nuna goyan baya a kan zirin Gaza.

Kakakin rundunar Yahya Saree ya ce a daren jiya litinin sojojin na Yaman sun kai hari filin tashi da saukar jiragen sama na Ben Gurion na Isra’ila da makami mai linzami guda biyu da suka hada da Zulfiqar mai gudun tsiya.

Ya kara da cewa hare-haren na goyon bayan Falasdinawa ne a Gaza.

Saree ya yi nuni da cewa, dakarun kasar Yemen sun kuma kai hari kan jirgin yakin Amurka Harry S.

Saree ya ce harin da aka kai kan jiragen ruwan yakin Amurka shi ne irinsa na biyu cikin sa’o’i 24 da suka gabata.

Ya ce an kai harin ne domin mayar da martani ga hare-haren da Amurka ke kaiwa kasar ta Yemen.

Saree ya kuma jaddada cewa za a ci gaba da gudanar da ayyukan adawa da Isra’ila har sai an daina ta’addancin gwamnatin tare da dage killacewar da aka yi wa Gaza.

A ranar 15 ga Maris, Amurka ta sanar da kai wani hari ta sama da ya yi sanadin mutuwar ‘yan kasar Yemen 53.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Kasar Iran Sun Ce Bazasu Dakatar Da Yaki ba Har Zuwa Samun Nasara A kan HKI

Babban kwamandan dokarun khatamul Ambiya (s) a nan birnin Tehran ya bayyana cewa sojojinsa zasu ci gaba da fafatawa da HKI har zuwa lokacinda zata dakatar da kawowa Iran yaki, ko kuma ta sami nasara a kansu,

Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto Janar Ali Shudmoni, yana fadar haka a yau Lahadi bayan da suke cilla makamai masu linzami da kuma jiragen yaki wadanda ake sarrafasu da nesa kan HKI a karon farko na rana, a cikin kwanaki uku da fara yakin.

Janar Shodmani ya kara da cewa zasu ci gaba da kaiwa yahudawan hare-hare har zuwa lokacinda zasu yi nadama sun daina yakin.

Kwamnatin ya bayyana cewa ya zuwa yanzu sun saminar kasar lalata cibiyoyin da jiragen yakin HKI suke shan makamashi wanda yake basu damar isa kasar Iran don kai hare-hare.  Banda haka akwai nasarori da dama da suka samu a hare-haren wadanda nan gaba zasu bayyana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dakarun IRGC Sun Kakkabo Jirahen Yakin HKI Wadanda Ake Sarrafasu Daga Nesa A Lardin Zanjan
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Ba’a Rufe Kofar Diblomasiyya Ba, Matukar HKI Ta Dakatar Da Kaiwa Kasar HKI
  • Sojojin Kasar Iran Sun Ce Bazasu Dakatar Da Yaki ba Har Zuwa Samun Nasara A kan HKI
  • NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka
  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
  • Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bude Kofofin Jahannama Ga Yahudawan Sahayoniyya
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba