Shugaban Majalisar Dokokin Lebanon Ya Yi Gargadi Akan Masu Tunanin Kulla Alakar Kasar Da HKI
Published: 24th, March 2025 GMT
Shugaban majalisar dokokin kasar Lebanon Nabih Barri ya jaddada cewa; HKI tana kokarin jefa Lebanon cikin tarkon kulla alaka da ita, yana mai jaddada cewa; Ko kadan Lebanon ba ta kama wannan hanyar ba.
Nabih Barri ya bayyana yadda wasu rahotanni daban-daban suke Magana akan cewa Amurka tana kai gwauro da mari, domin ganin an bude alaka kai tsaye a tsakanin Lebanon da HKI.
Shugaban majalisar dokokin kasar ta Lebanon ya ce, ko kadan kasar Lebanon ba ta tunanin kulla alaka da HKI.
Haka nan kuma ya yi ishara da tsagaita wutar yaki wacce a kodayaushe HKI take ketawa, yana mai tabbatar da cewa Hizbullah tana riko da ita, don haka ya yi kira ga Amurka da sauran bangarorin da suke a cikin tsagaita wutar da su yi matsin lamba ga HKI domin ta yi aiki da ita.
Bugu da kari Nabih Barri ya ce; Sojojin kasar ta Lebanon sun gama shiryawa domin shiga cikin kudancin tafkin Laitani, amma matsalar da ake fuskanta ita ce yadda Isra’ila take kin janyewa daga wasu yankuna a cikin Lebanon.
Nabih Barri ya kuma jaddada cewa; Kungiyar Hizbullah tana aiki da tsagaita wutar yakin, kuma ba ta keta ta ba ko kadan.
Shugaban Majalisar Dokokin kasar ta Lebanon ya kara da cewa; Duk da cewa HKI tana keta tsagaita wutar yaki, amma ko sau daya Hizbullah ba ta harba ko harsashi daya ba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: tsagaita wutar
এছাড়াও পড়ুন:
Martanin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Kan Ta’addancin ‘Yan Sahayoniyya ya Shiga Rana Ta Biyu
Martanin Iran game da ta’addancin haramtacciyar kasar Isra’ila na ci gaba a rana ta biyu
Ana ci gaba da mayar da martani mai girma na Iran game da harin da haramtacciyar kasar Isra’ila take kaiwa da makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka ciki.
‘Yan mintoci da suka gabata a zaman wani bangare na biyu na “Alkawarin Gaskiya Na 3”, Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta harba daruruwan makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka kan haramtacciyar kasar Isra’ila.
An harba wadannan makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka ciki da kuma jiragen sama masu saukar ungulu daga Tehran da sauran garuruwan kasar Iran a matsayin wani mataki na murkushe laifuffukan da yahudawan sahayoniyya suka aikata a kan yankunan Jamhuriyar Musulunci ta Iran, kuma a zaman wani bangare na biyu na “Alkawarin Gaskiya na 3”.
Kafofin yada labaran yahudawan sahayoniyya sun watsa rahoton tashin gobara da hayaki a birnin Haifa da ke arewacin Falasdinu da aka mamaye.
An ga wuta da hayaki na tashi bayan da makamai masu linzami na Iran sun afkawa matatar mai ta Haifa da ke arewacin Falasdinu da aka mamaye. Sannan a cewar bayanan farko, an kashe fiye da mutane 10 a Haifa.