Aminiya:
2025-11-02@19:45:34 GMT

Yadda ake noman gurjiya

Published: 23rd, March 2025 GMT

A tattaunawarsa da Aminiya wani manomin gurjiya, Malam Muhammad Dahiru Kanda ya bayyana cewa, ya shafe sama da shekara 25 yana noman gurjiya ba tare da ya taba samun wani tasgaro ba.

Ya kara da cewa, shi noman gurjiya na da muhimminci matuka domin kuwa yana samar wa duk mai yin sa babbar riba.

Mata sun ƙwace kasuwancin kayan lambu a Gombe Mutumin da girgizar ƙasa ta razana ya shekara 2 yana zaune a cikin kogo

A cewarsa, noman gurjiya noma ne da bai sai ka tanadar masa babbar gona ba, ya danganta ne ga yadda duk ka dauke shi, amma kuma ko da rabin hekta ka dauka, ka noma, matukar ka gyara ta to kuwa ko tantama babu in Allah SWT Ya so za ka same ta a yalwace.

Haka nan in har ya kasance ka samu kasar noma mai kyau kuma mai karfi za ka samu alheri sosai wajen samun biyan bukata.

A cewarsa a duk shekara yakan samu buhunhuna biyar zuwa 7 na gurjiya a ‘yar karamar gonarsa da ba ta kai eka guda ba, wadda wannan gurjiya in ya samu yakan biya bukatunsa da na iyalansa.

Ya ci gaba da cewa, noman gurjiya na bukatar hakuri da kuma shuka ta a kan lokaci daidai da lokacin da aka fara shuka gyada domin kuwa ita gurjiya kamar gyada ce, tana bukatar shiga cikin kasa tunda ‘ya’yanta a cikin kasa take zuba su.

Haka kuma, noman gujiya in son samu ne, ka kebance mata wurinta daban komai kakantarsa, maimakon ka shuka ta cikin gero ko dawa ko kuma hada ta cikin gyada domin in ka kebance wajen shuka ta daban, takan fi haihuwa da yawa sabanin shuka ta hade da wasu amfanin gona, kana tana bukatar a dan sa takin gida ko na zamani.

Don haka a gaskiya noman gujiya na da matukar muhimmanci domin kuwa yakan samar wa manoma alherin da ba ya misaltuwa, musamman ganin cewar gurjiya na da matukar daraja a kasuwa.

A yanzu haka buhun gurjiya mai nauyin kilo 50 kudinsa ya kai kimanin Naira dubu 55 zuwa dubu 60.

Baya ga haka kuma akwai bukatar manomi in ya zo shuka gurjiya, ya zabo iri mai kyau ba irin da zai tsumbure ba domin samun yalwarta.

“Yin hakan na daga cikin abin da ke taimaka min da ma sauran manoma wajen samun gurjiya mai yawa in lokacin cire ta ya yi, kuma matukar manomi na son amfana da ita a kaka, to kuwa ya guji yawan cire ta da danyentakarta tun ba ta kai ga kosawa ba, don sayarwa.

Sai dai in ba bukatar hakan ne ta taso ba, domin ni sau tari nakan hakura ne da cirar ta in tana danya illa daga lokaci zuwa lokaci nakan cira don kai wa iyali su dafa, su ci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gurjiya noman gurjiya

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi

Wasu ’yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun yi garkuwa da fasinjoji a cikin wasu motocin bas Toyota guda biyu a titin Itobe zuwa Ajegwu-Anyigba a Ƙaramar hukumar Ofu ta jihar Kogi.

An samu rahoton cewa, lamarin ya faru ne a ranar Alhamis da misalin ƙarfe 5 na asubahi a tsakanin ƙauyukan Ojiwo’-Ajengo da Mamereboh da ke kan babbar hanyar.

Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa

An ce masu garkuwa da mutanen sun yi amfani da wata tirela da aka kama wajen tare hanyar bayan shingen binciken jami’an tsaro, da ke kusa da wurin da lamarin ya faru.

Shedun gani da ido sun ce ɗaya daga cikin motocin bas ɗin mai lamba KG: KPA 622LG na kan hanyarta zuwa Abuja, tare da fasinjoji daga wata tashar mota a unguwar Ankpa da ke yankin Kogi ta Gabas.

Har yanzu ba a iya gano adadin fasinjojin da aka yi garkuwa da su ba zuwa yanzu, sai dai mun iya tabbatar da cewa ɗaya daga cikin motocin na ɗauke da fasinjoji ne daga yankin Ankpa, kamar yadda aka gano wasu takardu da wasu kayayyaki a wurin da lamarin ya faru suka bayyana.

“Motocin bas ɗin guda biyu suna kan hanyar Abuja ne a lokacin da suka ci karo da shingayen ’yan bindiga a safiyar ranar Alhamis. Dukkanin fasinjojin, ciki har da direban motocin bas ɗin biyu an yi awon gaba da su cikin daji,” in ji Unubi Ademu, wani mazaunin Achigili, a ƙauyen da ke maƙwabta.

Al’ummar yankin sun ƙara da cewa, jami’an tsaro da suka haɗa da sojoji da mafarauta da kuma ’yan banga suna ƙoƙarin magance lamarin.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar Kogi (PPRO), CSP William Aya bai amsa kira da saƙo ba lokacin da aka tuntuɓe shi har zuwa lokacin tattatara wannan rahoto.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Za Ku Hada Fab Biskit
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan