Aminiya:
2025-07-31@12:26:28 GMT

Majalisar Wakilai ta musanta karɓar kuɗi kan dokar ta-ɓaci a Ribas

Published: 22nd, March 2025 GMT

Majalisar Wakilai ta ƙaryata zargin da ake mata na karɓar cin hanci domin amincewa da dokar ta-ɓaci da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya ayyana a Jihar Ribas.

Ɗan majalisa mai wakiltar mazabar Gwaram a Jihar Jigawa, Hon. Yusuf Shittu Galambi, ya kare majalisar yayin da ake ta cece-kuce kan batun.

Gwamnati ta kama mutum 347 kan haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba Mace ta farko ta zama shugabar ƙasar Namibia

Wasu ƙungiyoyi na zargin majalisar da yin ƙasa a gwiwa wajen yanke hukunci kan lamarin.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, Galambi, ya ce babu gaskiya a zargin da ake yi cewa an tursasa ’yan majalisa ko an ba su na goro don su amince da matakin shugaban ƙasa.

Ya bayyana cewa yawancin mambobin majalisar sun goyi bayan matakin ne domin kare dimokuraɗiyya da kuma tsare muradun al’ummar Jihar Ribas.

“Mun yanke shawarar ne bisa kishin ƙasa, haɗin kan siyasa, zaman lafiya, da kare dimokuraɗiyya,” in ji shi.

Ya ce ya yi mamakin yadda wasu kafafen yaɗa labarai ke baza jita-jita cewa an tilasta musu su amince da dokar ta-ɓaci tare da karɓar daloli.

A cewarsa, ya kamata ’yan Najeriya su fahimci cewa ’yan majalisa suna aiki ne don ganin an samar da tawagar sulhu kafin wa’adin dokar ta-ɓacin ta ƙare.

Ya jaddada cewa dole ne a kare dimokuraɗiyya a Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Fubara Majalisar Wakilai Musantawa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Bukaci A Kara Inganta Aikin Titin Gabasawa

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta ba da shawarar a soke ko kara inganta aikin titin gina hanya mai tsawon kilomita biyar a karamar hukumar Gabasawa.

Wannan mataki ya biyo bayan karɓar rahoton da Kwamitin  Majalisar kan Harkokin Jinƙai da Rage Talauci ya gabatar dangane da ambaliyar da ta afku a Zakirai, cikin karamar hukumar ta Gabasawa.

Da yake gabatar da rahoton, Shugaban Kwamitin, Alhaji Sule Lawan Shuwaki, ya bayyana wasu muhimman shawarwari da suka hada da: Umurtar kamfanin da ke aikin gina hanyar da ya faɗaɗa magudanar ruwa a yankin da abin ya shafa da kuma gaggauta kai agajin gaggawa ga waɗanda ambaliyar ta shafa.

Sauran shawarwarin sun haɗa da tura tawagar ƙwararru daga ma’aikatun ayyuka da muhalli na jihar don gudanar da bincike da bayar da shawarwarin fasaha.

Bayan nazari da tattaunawa mai zurfi, majalisar ta amince da rahoton baki ɗaya tare da kiran gwamnatin jihar da ta gaggauta ɗaukar mataki domin rage tasirin ambaliya a Zakirai.

A wani sabon lamari kuma, majalisar ta yi kira ga gwamnatin jihar da ta gaggauta sake gina hanyar da ke haɗa Kwanar ‘Yan Mota zuwa Kwanar Bakin Zuwo zuwa Jakara, zuwa Kwanar Gabari a cikin karamar hukumar birnin Kano.

Wanda ya gabatar da kudirin, Honarabul Aliyu Yusuf Daneji, mai wakiltar mazabar Kano Municipal, ya jaddada cewa hanyar, musamman a kusa da kasuwar Kurmi, tana cikin matsanancin hali wanda ke kawo cikas ga zirga-zirga da kuma lalata harkokin kasuwanci.

Haka kuma, Alhaji Abdullahi Yahaya, mai wakiltar mazabar Gezawa, ya gabatar da kudiri na buƙatar gina titin kwalta daga Jogana zuwa Matallawa, Yamadi Charo da Daraudau.

Ya ce hanyar ba ta dadin bi a lokacin damina, inda al’ummar yankin ke ɗaukar matakin kansu ta hanyar cike ramuka da yashi da itace.

Kudirin ya samu goyon bayan Jagoran Masu Rinji a Majalisar, Alhaji Zakariyya Abdullahi Nuhu, tare da cikakken goyon bayan ‘yan majalisar baki ɗaya.

Sauran kudirori da aka amince da su a zaman sun haɗa da: Gina titi daga Dalawada zuwa Gazobi a karamar hukumar Tudun Wada da kuma sake gina hanyar Fanisau a Ungogo.

 

Daga Khadijah Aliyu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana
  • Za mu halasta kafa ƙasar Falasɗinu muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba — Birtaniya
  • Muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba za mu amince da kafa ƙasar Falasɗinu — Birtaniya
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Na Da Kwamitoci 30 Da Ke Sa Ido Kan Ma’aikatun Gwamnati
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • Kasar Iran Ta Musanta Yin Katsalandan A Tattaunawar Neman Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • An fara shigar da kayan agaji a Gaza
  • Tinubu ya bai wa ’yan ƙwallon Nijeriya mata kyautar kuɗi da gida da lambar yabo
  • Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Bukaci A Kara Inganta Aikin Titin Gabasawa