Aminiya:
2025-06-15@19:13:45 GMT

Muhimman ayyuka 8 a goman ƙarshe na Ramadan

Published: 20th, March 2025 GMT

A yayin da aka shiga kwana goman ƙarshe a watan Ramadan, ga tunarwar wasu muhimman ayyukan lada da ya kamata a dage da su a cikin watan mai alfarma.

Fitaccen malamin Musulunci, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, ya bayyana cewa riƙo da su yana da muhimmanci saboda tarin lada da aka tanadar wa mai aikata su:

Yadda Teloli Ke Cin Kasuwa A Azumin Bana Fursunoni 100 na neman afuwa a Kano Itikafi: Ana so mutum idan mutum yana da hali ana ya shiga Itikafi, inda da lazimci bautar Allah.

Mutum, namiji ko mace, na iya Itikafi na tsawon kwanakin ko na iya abin da ya sawwaka. Neman daren Lailatul Kadar: Mutum ya dage wajen kirdado da neman dacewa da daren Lailatul Kadari, ta hanyar gabatar da salloli da addu’o’i da sauran ayyukan ibada, musamman a dararen mara a goman karshen watan Ramadan. Sallah: Musamman Sallar Tarawihi da Tahajjud, baya ga yin sallolin farilla a cikin jam’i, da kuma yin nafilolin da ake yi kafin ko bayan sallolin na farilla. Karatun Al-Kur’ani: A dage a yawaita karatun Al-Kur’ani domin a cikin watan Ramadan aka saukar da shi, a daren Lailatul Kadar, cikin kwana goman karshe. Addu’o’i: A dage da addu’o’in neman garafa da rahamar Allah da aljannah da kuma dacewa da alherin duniya da lahira da kuma neman tsari daga wuta da kuma sharrin duniya da na lahira. Mutum na iya yin addu’a a lokutan da ake amsa addu’o’i kamar lokacin Sahur ko bude-bakin da lokacin da ake cikin azumin da cikin sujada ko a cikin sulusin karshe da dare da sauransu. Umrah: Hadisi ya nuna wanda ya yi Umra a cikin goman karshe na Ramadan zai samu ladar yin aikin Hajji tare da Manzon Allah (SAW). Zakka: Ana so duk Musulmi mai hali ya fitar da Zakkar Kono ya ba wa mabukata. Magidanci da da da hali zai fitar da sa’i daya (Mudun Nabi hudu) na hatsi, haka kuma zai fitar wa iyalansa da duk wanda yake ciyarwa. Ana iya fitarwa a bayar daga ranar 28 ga Ramadan har zuwa lokacin tafiya masallacin idi ranar Karamar Sallah. Kabbarori: Ana yin kabbarori daga bayan faduwar ranar jajibirin Karamar Sallah, har zuwa lokacin da za a idar da sallar idin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Goman Karshe kwana 10 Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin

Yayin taron shekara-shekara na tattaunawar CBD na shekarar 2025 da aka rufe a yau Juma’a 13 ga wata, mashawarci kana kwararre a hukumar kasuwancin kasar Sin ta kasar Birtaniya, kuma shugaban cibiyar bunkasa kasuwanci tsakanin Birtaniya da Sin mista John Mclean, ya bayyana yayin da yake hira da wakilin CMG cewa, kasuwar kasar Sin tana cike da damammaki, don haka dole ne ya shiga a dama da shi a cikinta. A ganinsa, yayin da ake tinkarar tashe-tashen hankula da rashin tabbaci a duniya, babbar baiwar da Sin take da ita, da muhalli mai aminci da bude kofa ga kowa, sun samarwa kamfanonin Birtaniya da ma duniya baki daya damammaki.

Tun bayan kafuwarsa a shekarar 2000 zuwa yanzu, taron ya kasance dandali da kasar Sin ke tattaunawa da kasashen duniya. A yayin taron bana, wakilai fiye da 6000 daga sassan siyasa, da kasuwanci, da ilimi da suka fito daga kasashe da yankuna fiye da 40 sun halarta. A lokacin gudanar da taron, wasu mahalartansa sun yi nuni da cewa, kasar Sin na da babbar juriya wajen raya tattalin arziki, da kuma babbar baiwar raya kasa. Haka kuma, gwamnatin Sin ta gaggauta raya sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko, lamarin da ya zuba sabon kuzari ga kamfanonin kasashen waje, ta yadda suke shiga a dama da su wajen yin ciniki a kasar Sin.

A yayin bikin bude taron, mahalartansa sun yi kira da a gina duniya mai tsabta, da kyawu, da dorewa cikin hadin gwiwa, duba da ganin kasar Sin ta ba da babbar gudummawa, ta kuma yi iyakacin kokari a fannin raya kasa ba tare da gurbata muhalli ba, da kuma rage fitar da sinadarin carbon. Alkaluma sun nuna cewa, yanzu haka kasar Sin tana daya daga cikin kasashen da suka fi saurin rage yawan makamashi mai dumama yanayi da suke amfani da shi da samun kyautatuwar iska, ta kuma dasa yawan bishiyoyi, da ciyayi da fadinsu ya kai rubu’i bisa jimillar fadin sabbin bishiyoyi da ciyayi na duniya baki daya, tare da kafa tsarin makamashin da ake sake amfani da shi mafi girma, kuma mafi saurin ci gaba a duniya, baya ga kafa tsarin masana’antu na sabbin makamashi mafi girma kuma cikakke a duniya. (Tasallah Yuan)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu
  • Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran
  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India