Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Samar da Dokar Shirye-Shiryen Matasa Da Ayyukan

 

Ministan ci gaban matasa, Ayodele Olawande, ya jaddada kudirin gwamnatin tarayya na karfafa matasa domin samar da zaman lafiya da ci gaban tattalin arzikin kasar nan.

 

Ministan ya ce ziyarar da ya kai jihar Sokoto na da nufin kara cudanya da matasa a cikin watan Ramadan da bayar da tallafi mai mahimmanci.

 

Olawande, wanda ya samu rakiyar Seyi Tinubu, ya jaddada mahimmancin shirye-shiryen da suka shafi matasa, ciki har da samar da dandalin tattaunawa kan ci gaban matasa na kasa.

 

Ya yi nuni da cewa, shugaban kasa Bola Tinubu da Gwamna Ahmed Aliyu suna da manufa daya na ci gaban matasa, ta yadda za a yi amfani da albarkatun da aka ware wa Sokoto yadda ya kamata.

 

Ministan ya kuma yaba da bullo da shirin ba da lamuni na dalibai, inda ya bayyana shi a matsayin wani gagarumin shiri na tallafawa daliban Najeriya.

 

Ya kuma ba da tabbacin cewa, akwai wasu shirye-shiryen da suka shafi matasa, inda Sokoto za ta ci gajiyar muhimman tsare-tsare a fannin noma, gidaje, da kuma shirye-shiryen horarwa.

 

Ya kuma kara ba da tabbacin cewa FG na kokarin samar da yanayi mai dacewa da matasan Najeriya za su ci gaba.

 

A nasa jawabin, gwamna Ahmed Aliyu na sokoto, ya bayyana ziyarar a matsayin wata shaida ga jajircewar da gwamnatin ta yi wajen karfafa matasa.

 

Ya yabawa Seyi Tinubu, wanda shine wanda ya assasa Renewed Hope Youth Empowerment Initiative, bisa gudunmawar da yake bayarwa a harkokin siyasa da ci gaban tattalin arziki, yana mai kira gare shi da ya mika shirye-shiryensa ga matasan Sokoto.

 

Gwamnan ya kuma bayyana irin kokarin da gwamnatin sa ke yi na tallafa wa matasa da suka hada da nada matasa a manyan mukamai a gwamnati da samar da ilimi kyauta ga dukkan dalibai ba tare da la’akari da addini ko kabila ba.

 

Ya yabawa Tinubu kan irin ayyukan alheri da yake yi a cikin watan Ramadan, musamman ga marasa galihu.

 

Tun da farko, Seyi Tinubu ya bayyana kudirinsa na ci gaban matasa a Sakkwato, inda ya yi alkawarin cewa gidauniyarsa za ta ci gaba da tallafa wa ayyuka a fadin kananan hukumomin jihar 23.

 

Nasir Malali

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 

Fadar Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa nan da wasu kwanaki Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai gana da takwaransa na Amurka, Donald Trump, domin tattaunawa kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya.

Mai ba wa Shugaba Tinubu shawara na musamman kan yaɗa manufofi, Daniel Bwala, ne ya tabbatar da hakan a cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X.

Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan

A cewar Daniel Bwala, shugabannin biyu — Tinubu da Trump — sun yi tarayya da juna kan fahimta ta haɗin kai wajen yaƙi da ta’addanci da duk wata barazana ga bil’adama.

“A bayan nan Shugaba Trump ya taimaka wajen ba da izinin sayar wa Nijeriya makamai, kuma Shugaba Tinubu ya yi amfani da damar yadda ya kamata wajen yaƙi da ta’addanci, kuma muna da sakamakon da za mu iya nunawa,” in ji Bwala.

Ya ƙara da cewa duk wani saɓanin fahimta kan ko ‘yan ta’adda a Nijeriya na kai hari ne ga Kiristoci kaɗai ko kuma mabiyan addinai daban-daban, “za a tattauna kuma a warware su” a yayin ganawar shugabannin biyu, wadda za ta gudana “ko dai a Fadar Shugaban Kasa ta Abuja, ko a Fadar White House da ke Washington.”

Sanarwar ta zo ne bayan barazanar Shugaba Trump ta kai farmaki a Nijeriya, inda ya umarci Ma’aikatar Yaƙin Amurka ta Pentagon da ta fara tsara yadda za a kai hari kan ƙasar, saboda abin da ya kira “kisan gillar da ake yi wa Kiristoci” a Nijeriya.

A cikin wani saƙo da ya wallafa a Truth Social, Trump ya ce Amurka “a shirye take ta turo sojojinta da manyan makamai zuwa Nijeriya don kare Kiristoci,” yana mai cewa idan gwamnatin Nijeriya ta ci gaba da bari ana kashe Kiristoci, Amurka za ta dakatar da dukkan tallafin da take bai wa Nijeriya, kuma “mai yiwuwa ta shiga ƙasar don kawar da ‘yan ta’adda masu zafin kishin Musulunci.”

Barazanar Trump ta jawo cece-kuce bayan ya yi iƙirarin cewa an kashe Kiristoci aƙalla 3,100 a Nijeriya, ba tare da ya bayyana takamaiman inda ya samo waɗannan alƙaluman ba.

Sai dai a martanin da ya mayar, Shugaba Bola Tinubu ya jaddada cewa Nijeriya tana nan daram a matsayin ƙasa mai kiyaye dimokuraɗiyya, wadda kundin tsarin mulkinta ke tabbatar da ‘yancin yin addini da haƙuri tsakanin mabambantan addinai.

“Tun daga shekarar 2023, gwamnatinmu tana gudanar da tattaunawa sosai da shugabannin addinai na Kiristanci da Musulunci, tare da ci gaba da magance matsalolin tsaro da ke shafar jama’a daga addinai da yankuna daban-daban,” in ji Tinubu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
  • Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan