Muƙarraban Uba Sani ne suka sace tsohon Kwamishina na – El-Rufai
Published: 14th, March 2025 GMT
Tsohon gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai, ya fasa baragurbin ƙwai kan zargin sace Jafaru Sani, tsohon Kwamishina a gwamnatinsa.
El-Rufai, wanda ya mulki Jihar Kaduna daga 2015 zuwa 2023 kafin ya miƙa mulki ga Sanata Uba Sani, wanda shi ne ɗan takarar da ya fi so ya gaje shi, ya bayyana wannan batu ne a shafinsa na Facebook da aka tantance sahihancinsa a ranar Alhamis.
A cewarsa, an tsare tsohon Kwamishinan na shi ne a kurkuku ba bisa ƙa’ida ba.
El-Rufai ya ce, yana da tabbacin ana cin zarafin abokin nasa ne saboda ya fice daga Jam’iyyar APC zuwa SDP.
“An sace abokin aikinmu kuma tsohon kwamishina mai ƙwazo a zamanin mulkin El-Rufai, Malam Jafaru Sani, an sace shi ne a Kaduna da rana tsaka, yana ta hannun ‘yan fashin dajin Uba Sani da ke cewa su ’yan sanda ne!
“An tsare Jafaru a kurkuku ba tare da wata takardar sammaci daga ‘yan sanda ko ta tuhuma daga Ma’aikatar Shari’a ta Jiha ba.
“Bayan bincike, mun gano cewa ana zarginsa da safarar kuɗi. Amma ainihin laifin Jafaru shi ne ficewarsa daga APC zuwa SDP.
“Wannan salon zaluncin iri ɗaya ne da wanda aka taɓa yi wa wani abokinmu, Bashir Saidu, wanda aka sace a ranar 31 ga Disamba, 2024, aka tsare shi na tsawon kwanaki 50 kafin a bayar da belinsa!
“Rawar da wasu alƙalai ke takawa a shari’ar Kaduna abu ne mai matuƙar damuwa. Muna sa ido kuma muna jira domin babu wani yanayi da zai dawwama, kuma ranar hisabi za ta zo.”
Har yanzu gwamnatin Jihar Kaduna ba ta mayar da martani kan waɗannan zarge-zargen da El-Rufai ya yi ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamna Uba Sani
এছাড়াও পড়ুন:
ICPC Ta Gurfanar Da Ma’aikacin Kotu Bisa Badakalar Naira Miliyan 9.2
Abdulazeez pleaded not guilty to the two-count charge. Abdulazeez ya ki amsa laifin da ake tuhumarsa da su biyu.
Bayan rokon da ta yi, lauyan ICPC, Hamza Sani, ya bukaci kotun ta dage sauraron karar zuwa ranar 13 ga watan Yuni, 2025, domin masu gabatar da kara su gabatar da shaidu.
Sai dai daga baya kotun ta ba da ranar sannan ta dage sauraron karar zuwa ranar 20 ga watan Yunin 2025 domin sauraron karar.
Lauyan wanda ake tuhuma ya nemi a ba shi belin, wanda ICPC ba ta yi adawa da shi ba.
Mai shari’a Iheabunke ya bayar da belinta a kan kudi naira miliyan 10, tare da mutane biyu da za su tsaya mata.
Ya ce dole ne wadanda ake kara su mallaki kadarorin da ke karkashin ikon kotun, sannan su mika takardun mallakar asali ga magatakardar kotun don tantancewa, sannan wanda ake kara ya sanar da kotu a hukumance kafin tafiya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp