“Yan Ta’addan Syria Suna Boye Gawawwakin Mutanen Da Su Ka Yi Wa Kisan Gilla
Published: 11th, March 2025 GMT
Rahotannin da suke fitowa daga Syria sun ambaci cewa kungiyoyin ‘yan ta’adda da suke da alaka da shugaban gwamnatin Syria, Julani sun fara dauke gawawwakin mutanen da su ka yi wa kisan kiyashi zuwa wasu wurare da ba a san ko’ina ne ba.
Saboda yadda fushin kasashen duniya yake karuwa akan kisan kiyashin da ‘yan ta’adda su ka yi a gabar ruwan Syria, masu mulki a Damascuss suna boye gawawwakin gabanin isar tawagar MDD zuwa yankin.
Mafi yawancin mutanen da aka yi wa kisan gillar a yankin gabar ruwan Syria, fararen hula ne wadanda aka fito da su daga cikin gidajensu,yayin da wasu kuma aka yi musu kisan gilla a gaban iyalansu.
Ya zuwa shekaran jiya ana maganar cewa an kashe mutanen da sun kai 1,700.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Mutum 2 sun mutum a ƙoƙarin ciro wata daga masai a Kano
Wasu mutum biyu sun rasu a cikin masai a yayin da suke ƙoƙarin ciro wata ƙaramar waya da ta faɗa a ciki shaddar a yankin Ƙaramar Hukumar Albashi ta Jihar Kano.
Hukumar kashe gobara ta jihar ta ce mutanen biyu sun gamu da ajalinsu ne a ranar Asabar a unguwar Bazabe da ke ƙaramar hukumar.
Kakakin hukumar, Saminu Yusif Abdullahi, ya sanar cewa a safiyar ranar Asabar ne aka sanar da ofishin kwana-kwana ta samu kiran gaggawa game da lamarin.
Ya bayyana cewa wani ɗan shekara 40 ya shiga masai domin ciro wayarsa da ta faɗa a ciki, amma sai ya maƙale a ciki.
A sakamakon wani mai suna Ibrahim ya shiga domin ciro shi, amma bayan ya yi nasarar sanya masa igiya, sai shi ma ya yanke jiki ya fadi a ciki.
Daga baya hukumar ta yi nasarar fito da su ta kai asibiti inda aka tabbatar cewa sun rasu.
Hukumar ta mika gawarwakinsu ga Babban Ofishin ’Yan Sanda da ke Ƙaramar Hukumar Albasu domin ci gaba bincike da sauran abubuwan da suka dace.
Daga ƙarshe Hukumar ta buƙaci jama’a da su daina jefa kansu a cikin haɗari su rika neman taimako daga ƙararru a duk lokacin da wani abu na gaggawa ya taso.