Blatter da Platini sun sake gurfana a kotu kan zargin cin hanci
Published: 10th, March 2025 GMT
Tsohon Shugaban Hukumar Kwallon Kafa ta Duniya (FIFA) Sepp Blatter, da tsohon Shugaban Hukumar Kwallon Kafar Turai (UEFA) Michel Platini, sun sake gurfana a gaban wata kotu a kasar Switzerland, domin sake duba tuhume-tuhumen da ake musu na cin hanci da rashawa.
Wata kotun daukaka kara ta musamman da ke zama a Muttenz ce ta saurari bukatar da ofishin babban mai shigar da kara na kasar ya kabatar, na sake dawo da tuhume-tuhumen da ake yi wa Blatter, wanda yake cika shekaru 89 a yau ranar 10 ga wannan wata na Maris, da kuma Platini mai shekaru 69.
Blatter, ya yi kokarin amfani da damar wajen wanke kansa, daga zargin cin hanci da aka yi musu da Platini, shahararren tsohon dan wasan Faransa.
A lokacin da ya ke gabatar da jawabi a makon da ya gabata, Blatter ya bayyana shari’ar a matsayin bita-da-kulli, saboda kotun baya ta tabbatar da sahihancin kwantiragin da ke tsakaninsa da Platini.
Don haka ya ce ya na da tabbacin ita ma wannan kotun za ta tabbatar da hakan.
A shekarar 2022 ce dai kotu ta wanke su kan zargin cin hanci na dala miliyan 2 da dubu dari da ake musu, bayan shafe shekaru bakwai ana shari’ar.
Blatter dai ya jagoranci hukumar FIFA ne daga tsakanin shekarar 1998 zuwa 2015, inda aka sa ran Platini ya gajeshi a shugabancin hukumar.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Zargi: ’Yan sanda sun musanta sace tsohon Kwamishinan El-Rufai
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, ta ƙaryata zargin da Tsohon Gwamna Nasir El-Rufai ya yi cewa jami’an tsaro sun sace tsohon Kwamishinansa, Jafaru Sani.
El-Rufai ya yi wannan iƙirari ne a shafinsa na sada zumunta cewa an ɗauke tsohon Kwamishinan kamar fursuna ba tare da bin ƙa’idojin doka ba.
Direba ya murƙushe yarinya ta mutu a artabu da jami’an tsaro a Edo Cutar sanƙarau ta kashe sama da mutum 50 a Sakkwato da KebbiYa yi zargin cewa wata “ƙungiyar masu garkuwa da mutane” da ke da alaƙa da Gwamna Uba Sani ce ke da alhakin ɗauke tsohon Kwamishinan.
Da yake mayar da martani, kakakin ’yan sandan jihar, DSP Mansir Hassan, ya bayyana zargin a matsayin ƙarya.
“Babu wata ƙungiyar masu garkuwa da mutane a cikin Rundunar ’Yan Sandan Najeriya.
“Mu hukuma ce da ke aiki bisa kundin tsarin mulki don tabbatar da doka da oda,” in ji shi.
Ya buƙaci ’yan siyasa su guji yaɗa labaran da ba su da tushe.
“Yi wa jami’an tsaro ƙarya na iya haifar da ruɗani da kuma rage martabarsu. Idan mutum yana da ƙorafi, ya bi hanyar shari’a maimakon yaɗa kalaman da za su tayar da fitina,” a cewarsa.