Aminiya:
2025-07-02@02:23:48 GMT

Blatter da Platini sun sake gurfana a kotu kan zargin cin hanci

Published: 10th, March 2025 GMT

Tsohon Shugaban Hukumar Kwallon Kafa ta Duniya (FIFA) Sepp Blatter, da tsohon Shugaban Hukumar Kwallon Kafar Turai (UEFA) Michel Platini, sun sake gurfana a gaban wata kotu a kasar Switzerland, domin sake duba tuhume-tuhumen da ake musu na cin hanci da rashawa.

Wata kotun daukaka kara ta musamman da ke zama a Muttenz ce ta saurari bukatar da ofishin babban mai shigar da kara na kasar ya kabatar, na sake dawo da tuhume-tuhumen da ake yi wa Blatter, wanda yake cika shekaru 89 a yau ranar 10 ga wannan wata na Maris, da kuma Platini mai shekaru 69.

NAJERIYA A YAU: Ladan Da Mai Aikin Ƙarfi Yake Samu A Lokacin Azumi PDP ta sake ɗage babban taronta zuwa Mayun 2025

Blatter, ya yi kokarin amfani da damar wajen wanke kansa, daga zargin cin hanci da aka yi musu da Platini, shahararren tsohon dan wasan Faransa.

A lokacin da ya ke gabatar da jawabi a makon da ya gabata, Blatter ya bayyana shari’ar a matsayin bita-da-kulli, saboda kotun baya ta tabbatar da sahihancin kwantiragin da ke tsakaninsa da Platini.

Don haka ya ce ya na da tabbacin ita ma wannan kotun za ta tabbatar da hakan.

A shekarar 2022 ce dai kotu ta wanke su kan zargin cin hanci na dala miliyan 2 da dubu dari da ake musu, bayan shafe shekaru bakwai ana shari’ar.

Blatter dai ya jagoranci hukumar FIFA ne daga tsakanin shekarar 1998 zuwa 2015, inda aka sa ran Platini ya gajeshi a shugabancin hukumar.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

A yau Talata ne gwamnatin yankin musamman na Hong Kong na kasar Sin ya gudanar da bikin daga tuta, da bikin murnar cika shekaru 28 da dawowar yankin musamman na HK karkashin ikon kasar Sin.

Da yake jawabi yayin taron, kantoman yankin Lee Ka Chiu John, ya ce tun bayan kama aikinsa, gwamnati mai ci a HK, ta ci gaba da aiwatar da sauye-sauye don gina yanki mai tsaro da daidaito, tare da zage damtse wajen gina tattalin arziki, da bunkasa zamantakewar al’ummarsa, kuma sannu a hankali matakan na haifar da mai ido.

Lee ya ce, a nan gaba, zai yi aiki tukuru wajen tabbatar da samun ci gaba mai inganci, da managarcin yanayin tsaro, kana zai gaggauta bunkasa yankin arewacin yankin, da kara azamar kyautata rayuwar jama’ar HK. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin
  • Za mu shige gaba idan aka dawo da tattauna shirin nukiliyar Iran — EU
  • Kotu A Kasar Iraki Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wadanda Suka Kashe Ayatullahi Baqir Sadr
  • An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS
  • Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa
  • Kotu za ta duba yiwuwar ba da belin Tukur Mamu a ranar 22 ga watan Yuli
  • Magidanci ya kashe matarsa da adda a Yobe
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4
  • Mutanen Sakkwato na neman ɗaukin gwamnati game da Bello Turji
  • Nijeriya ce kasa ta 12 mafi talauci a duniya — IMF