Aminiya:
2025-12-04@14:45:50 GMT

Blatter da Platini sun sake gurfana a kotu kan zargin cin hanci

Published: 10th, March 2025 GMT

Tsohon Shugaban Hukumar Kwallon Kafa ta Duniya (FIFA) Sepp Blatter, da tsohon Shugaban Hukumar Kwallon Kafar Turai (UEFA) Michel Platini, sun sake gurfana a gaban wata kotu a kasar Switzerland, domin sake duba tuhume-tuhumen da ake musu na cin hanci da rashawa.

Wata kotun daukaka kara ta musamman da ke zama a Muttenz ce ta saurari bukatar da ofishin babban mai shigar da kara na kasar ya kabatar, na sake dawo da tuhume-tuhumen da ake yi wa Blatter, wanda yake cika shekaru 89 a yau ranar 10 ga wannan wata na Maris, da kuma Platini mai shekaru 69.

NAJERIYA A YAU: Ladan Da Mai Aikin Ƙarfi Yake Samu A Lokacin Azumi PDP ta sake ɗage babban taronta zuwa Mayun 2025

Blatter, ya yi kokarin amfani da damar wajen wanke kansa, daga zargin cin hanci da aka yi musu da Platini, shahararren tsohon dan wasan Faransa.

A lokacin da ya ke gabatar da jawabi a makon da ya gabata, Blatter ya bayyana shari’ar a matsayin bita-da-kulli, saboda kotun baya ta tabbatar da sahihancin kwantiragin da ke tsakaninsa da Platini.

Don haka ya ce ya na da tabbacin ita ma wannan kotun za ta tabbatar da hakan.

A shekarar 2022 ce dai kotu ta wanke su kan zargin cin hanci na dala miliyan 2 da dubu dari da ake musu, bayan shafe shekaru bakwai ana shari’ar.

Blatter dai ya jagoranci hukumar FIFA ne daga tsakanin shekarar 1998 zuwa 2015, inda aka sa ran Platini ya gajeshi a shugabancin hukumar.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar

Shugaban Ƙungiyar Iyaye na Jami’ar MAAUN, Alhaji Mustapha Balarabe, ya ƙaryata rahotannin da ke cewa jami’ar ta yanke wasu kuɗi masu yawa domin yaye ɗalibai.

A wata sanarwa da ya fitar tare da sakataren ƙungiyar, Hajiya Habiba Sarki, ya ce koken da aka kai wa PCACC da kuma rahotannin da aka wallafa ba su da tushe.

Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a ’Yan sanda sun gano zinaren N23m bayan shekara 13 da ɓacewarsu a Borno

Ya bayyana zargin a matsayin yunƙurin ɓata wa jami’ar suna.

Ya ce MAAUN na daga cikin jami’o’in masu zaman kansu mafi sauƙin farashi a Kano, kuma tana ba da ingantaccen ilimi.

“MAAUN na ɗaya daga cikin jami’o’i masu zaman kansu masu sauƙin farashi a Kano, tana ba da ingantaccen ilimi tare da ƙayatattun gine-gine.

“Wasu jami’o’in a jihar suna cajin kuɗin makaranta ninki uku a kan na MAAUN, amma ba a jin kukan kowa game da su. Me ya sa sai MAAUN?

“Idan ɗalibi ya biya kuɗin makaranta na tsawon shekaru huɗu, me ya sa za a ga laifi idan aka nemi ya biya kuɗin yayewa a jami’a mai zaman kanta?

“Wannan ba wani sabon abu ba ne. Wannan batu gaba ɗaya na nuna wata maƙarƙashiya ce da ke nufin ɓata suna da barazana daga wanda ba a san ko waye ba da yake iƙirarin cewa yana kare muradun ɗalibai da iyaye,” in ji shi.

Ya kuma yi tambaya: “Me ya haɗa MAAUN da hukumar PCACC a kan wannan batu?”

A ƙarshe, ya shawarci wanda ya kafa jami’ar da ya ci gaba da jajircewa wajen samar da ilimi mai inganci.

A gefe guda kuma, ya yaba masa saboda ƙin ƙara kuɗin makaranta duk da halin matsin tattalin arziƙi da ya sa wasu jami’o’i ƙara ƙudinsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa
  • ’Yan sanda sun kama mutum 28 kan zargin lalata mata da yara a Yobe
  • An tsare tsohuwar shugabar kula da manufofin ketare ta EU Mogherini bisa badakalar cin hanci
  • Nijar ta maka kamfanin hakar uranium na Faransa Orano kotu
  • Masar Ta Sanar Da Tattaunawa Da Amurka Don Shirya Sake Gina Gaza
  • MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar