Hukumar Raya Arewa maso Yamma Ta Kai Ziyara Jihar Jigawa
Published: 8th, March 2025 GMT
Gwamnatin jihar Jigawa ta ja hankalin shugabannin Hukumar Raya Arewa Maso Yamma da su yi aiki bisa gaskiya da rikon amana domin samun goyon bayan gwamnonin shiyyar.
Gwamna Umar Namadi ya yi kiran ne a lokacin da ya karbi bakuncin shugabannin hukumar karkashin jagorancin shugabanta Alhaji Lawal Sama’ila Yakawada a gidan gwamnati da ke Dutse.
Ya ce, Hukumar Raya Arewa maso Yamma, ita ce mafi girma a cikin shiyyoyin kasar nan, a don haka bai kamata a fuskanci wasu matsaloli ba daga gareta.
Namadi ya bukace su da su mai da hankali da jajircewa, tare da yin aiki da abubuwan da gwamnoni suka sa gaba domin samun nasara.
Tun da farko, Shugaban Hukumar, Alhaji Lawal Sama’ila Yakawada ya ce sun je ziyarar ce da nufin gabatar da kansu a hukumance da kuma neman tallafi da karfafa gwiwar gwamnati.
A cewarsa, an kafa hukumar ne da amincewar gwamnonin yankin, don haka ya zama wajibi a nemi goyon bayansu.
“Jihar Jigawa jiha cceda ke noma tare da jajircewa, don haka mun ga ya dace mu fara zuwa nan bayan mun ziyarci shugaban kungiyar gwamnonin Arewa, domin samun goyon baya,” in ji Samaila
Alhaji Sama’ila Yakawada ya ce tuni hukumar ta samu bayanai kan bangarorin hadin gwiwa da jihar Jigawa domin bunkasa tattalin arziki da zamantakewa.
Ya bayyana Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Yamma a matsayin hukumar da ta fi kowacce hukuma a sauran ayyuka da jihohi bakwai, inda ya ce akwai kalubale da dama.
Shugaban, ya yabawa Gwamna Umar Namadi, bisa kokarinsa na yakar matsalolin da suka addabi al’umma, tun kafin ya hau kujerar gwamnan jihar Jigawa, kamar yadda bayanai suka nuna.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
“Iyakar kasa ba wai kawai yanki ne na tsaro ba. Yanki ne na al’adu; yanki ne na tarihi; haka nan ma yanki ne na tattalin arziki. Kula da shige da fice na da matukar amfani ga ci gabanmu. Wajibi ne Nijeriya ta zuba jari a kan kula da nau’in mutanen da take tacewa wajen shiga kasa da kuma irin mutanen da muke tacewa wajen fita daga kasa.
“Dole ne mu yi nazarin nau’in ayyukan da bakin-haure ke yi da kuma yadda suke shafar tattalin arzikinmu. Muna bukatar tsame mutanen da ke kawo cikas ga ci gabanmu”, in ji Babandede.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA