HausaTv:
2025-07-31@18:30:00 GMT

OIC Ta Yi Maraba Da Shirin Gwamnatocin Larabawa Na Sake Gina Zirin Gaza

Published: 8th, March 2025 GMT

Babban sakataren kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC, Hussein Ibrahim Taha, ya bayyana goyon bayan kungiyar ga shirin Larabawa na sake gina zirin Gaza.

Kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta gudanar da wani zama na musamman na majalisar ministocin harkokin wajen kasashe mambobi a kungiyar, taron da ya gudana a birnin Jeddah na kasar Saudiyya a wannan  Juma’a, inda suka tattauna halin da ake ciki dangane da ayyukan wuce gonad a iri na Isra’ila a Falastinu.

A cikin jawabinsa, Sakatare-Janar na Kungiyar Hadin Kan Musulunci ya tabbatar da goyon bayansa ga shirin sake gina zirin Gaza, wanda taron kolin kasashen Larabawa ya amince da shi, tare da jaddada hakkin al’ummar Palasdinu na ci gaba da zama a cikin kasarsu.

Baya ga haka kuma ya yi gargadi dangane da hadarin da ke tattare da matakan da Isra’ila take shirin dauka na korar Falastinawa daga yankunansu a Gaza, da kuam ammaye wasu yankuna a gabar yammacin kogin Jordan, yana mai cewa kungiyar OIC ba za ta taba  amincewa da hakan ba.

Babban magatakardar ya jaddada cewa, ba za a iya raba ko kuma maye gurbin hukumar ba da agaji ta Majalisar Dinkin Duniya a Falasdinu wato (UNRWA) da kuma muhimmiyar rawar da take takawa wajen yi wa miliyoyin ‘yan gudun hijirar Falasdinawa hidima ba, yayin da ya jaddada bukatar a rubanya tallafin siyasa da kudade ga wannan hukumar.

Babban magatakardar ya yi kira da a kara kaimi wajen aiwatar da yarjejeniyar tsagaita bude wuta, da janyewar sojojin mamaya gaba daya daga Gaza, da kuma isar da kayayyakin jin kai ga al’ummar yankin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanin NNPCL ya sake haka sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani

Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) ya sanar da sake haka sabbin rijiyoyin man fetur guda hudu yankin Kolmani na jihar Bauchi, kamar yadda Darakta a kamfanin, Yusuf Usman ya tabbatar.

Daraktan ya kuma sake jaddada aniyar kamfanin ta ganin ya fara aikin hako danyen man fetur a Arewacin Najeriya.

Samar da makamashi mai tsafta na zamani shi ne fatanmu — Guterres Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura

Ya bayyana hakan ne ranar Laraba a Kaduna a rana ta biyu ta taron tattaunawa tsakanin gwamnati da jama’a da Gidauniyar Tunawa da Ahmadu Bello ta shirya.

Daraktan ya ce, “Ya zuwa yanzu, NNPCL ya tono sabbin rijiyoyin danyen man fetur guda hudu a yankin Kolmani na jihar Bauchi, kuma yan kan aikin tantance fasahar da ta fi dacewa a yi aiki da ita a mataki na gaba a aikin.

“A wani yunkurinmu kuma na taimaka wa shirin Shugaban Kas ana komawa amfani da ababen hawa masu amfani da makamashin iskar gas a maimakon man fetur, yanzu haka ana can ana aikin gina tashoshin canza motoci zuwa masu amfani da gas na CNG da LNG,” in ji shi.

Ya ce da zarar an kammala aikinsu, ana sa ran tashoshin za su taimaka wajen bunkasa samuwar gas din kuma cikin sauki a Arewacin Najeriya.

Yusuf ya kuma zayyana wasu muhimman ayyuka da nasarorin da kamfanin ya samu a Arewacin Najeriya da ma sauran sassan kasar a karkashin mulkin Shugaban Kasa Bola Tinubu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa ta horas da malamai 20,000 fasahar sadarwar zamani
  • Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki
  • NNPCL ya sake haƙa sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
  • Kamfanin NNPCL ya sake haka sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
  • Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka
  • Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa
  • Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa