Najeriya ta kama hanyar gyaruwa – Remi Tinubu
Published: 7th, March 2025 GMT
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta shirya buɗa-baki a Fadar Gwamnati da ke Abuja, inda ta tabbatar wa ’yan Najeriya cewa ƙasar nan na kan hanya gyaruwa nan ba da jimawa ba.
A yayin jawabinta, ta jaddada muhimmancin tausayi da jin-ƙai a tsakanin rayuwar ɗan adam.
Wani mutum ya yanke jiki ana salla a Masallaci, ya rasu a asibiti Dakatarwa: Har yanzu ni Sanata ce — NatashaTa buƙaci kowa ya kasance mai aikata alheri tsakaninsa da Allah, ba don neman yabo ko amincewar mutane ba.
A yayin buɗa-bakin, Farfesa Azeezat Adebayo, Shugabar Sashen Nazarin Addinin Musulunci na Jami’ar Ilorin, ta bayyana cewa tausayi da jin-ƙai su ne ginshiƙai na kyakkyawar rayuwa a tsakanin al’umma.
Ta tunatar da mahalarta buɗa-bakin cewar watan Ramadan lokaci ne na koyon kyawawan ɗabi’u, kuma ana buƙatar a aikata alheri ga kowa, ba wai ga Musulmai kaɗai ba.
Daga cikin manyan baƙi da suka halarci buɗa-bakin akwai Uwargidan Tsohon Shugaban Ƙasa, Dame Patience Jonathan da matar Mataimakin Shugaban Ƙasa.
Sauran sun haɗa da matan gwamnonin jihohi, ministoci mata, matan ministoci da matan shugabannin hukumomin tsaro.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Buɗa baki gyara Najeriya Ramadan shan ruwa Uwargidan Tinubu
এছাড়াও পড়ুন:
An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp