Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya Ta Jinjinawa Gwamnatin Jigawa Bisa Wanzar Da Zaman Lafiya
Published: 7th, March 2025 GMT
Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta yabawa gwamnatin jihar Jigawa bisa yadda ta nuna damuwarta kan harkokin tsaro a jihar.
Mataimakin Sufeta na ‘yan sanda mai kula da shiyya ta daya, AIG Ahmed Ammani, ya bayyana haka a lokacin da ya kai wa Gwamna Umar Namadi ziyarar ban girma a gidan gwamnati dake Dutse babban birnin jihar Jigawa.
AIG Ammani ya yaba da dimbin tallafin da Gwamna Namadi ke bai wa ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro da ke aiki a jihar.
Ya bayyana jihar Jigawa a matsayin daya daga cikin jihohin kasar nan masu zaman lafiya.
A cewarsa, tun da ya samu mukamin AIG mai kula da shiyya ta 1, bai taba samun rahoton manyan laifuka daga rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ba, yana mai alakanta hakan da kokarin da gwamnan ke yi na tabbatar da zaman lafiya a jihar.
Hakazalika AIG ya yi amfani da damar wajen jajantawa gwamnan bisa rasuwar mahaifiyarsa da dansa, inda ya yi addu’ar Allah Yamusu rahma.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Rundunar Yan Sanda jihar Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Sanda A Kano Sun Kama Kasurgumin Dan Fashin Nan Barga Da Wasu Mutum 14
Rundunar ‘Yan Sanda a Jihar Kano ta samu nasarar kama mutane 15 da ake zargi da laifuka daban-daban, ciki har da wani kasurgumin dan fashi da makami mai suna Mu’azu Barga, a wani samame da aka lakaba wa suna “Operation Kukan Kura”.
Mai magana da yawun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Kano.
Ya ce samamen, wanda dakaru na musamman suka gudanar a unguwannin Sheka, Ja’oji, da Kurna a ranar 26 ga Yulin 2025, na da nufin gano da kuma hana aikata laifuka, bisa umarnin Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, IGP Kayode Adeolu Egbetokun.
Kiyawa ya bayyana cewa, wadanda aka kama ‘yan tsakanin shekaru 14 ne zuwa 28, kuma an same su da wayoyin salula guda hudu da suka sace daga hannun mutane daban-daban.
“Wadanda ake zargin sun amsa laifin aikata sata da fashi, musamman satar wayoyin salula,” In ji shi.
“Mu’azu Barga, wanda ake zargi da kasancewa barawo a lokuta da dama, yana daga cikin wadanda aka kama. Ana danganta shi da laifukan fashi da makami, da kuma. jagorantar hare-hare masu tayar da hankali da fada tsakanin kungiyoyin daba a cikin birnin Kano.”
Kiyawa ya kara da cewa, Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya ayyana yaki da duk wani nau’in laifi na daba, tare da jaddada kudurin rundunar na tabbatar da zaman lafiya da tsaro a jihar.
Ya bayyana godiyar rundunar bisa goyon bayan jama’a, tare da yin kira da su ci gaba da bayar da rahoton duk wani motsi ko mutum da suke zargi da aikata laifi, a ofishin ‘yan sanda mafi kusa.
Abdullahi Jalaluddeen