Yayin da watan Ramadan ya shiga kwana na 6, masu lura da al’amura da dama na kokawa kan tsadar kayan marmari a Kano, wanda suke ganin wani muhimmin bangare ne na karin kumallo da ake yi a sahur da kuma lokacin buda baki.

 

Malam Bello Ibrahim da Abdulmajeed Baba, masu amfani da ’ya’yan itatuwa musamman a lokacin azumin Ramadan, a wata tattaunawa da suka yi da gidan rediyon Najeriya, sun bayyana rashin jin dadinsu da tashin gwauron zabi.

 

 

‘Ya’yan itatuwa na da matukar muhimmanci ga lafiyar mu a lokacin azumi, amma farashin na kara zama wanda ba zai iya jurewa ba,” in ji su.

 

Malam Ado Shehu, jami’in hulda da jama’a na kasuwar ‘ya’yan itacen Naibawa, ya danganta tsadar kayan marmari da tsadar sufuri.

 

 

Sai dai wasu masu sayar da ‘ya’yan itace a kasuwar sun yi nuni da karancin kayan masarufi a matsayin babban dalilin tashin farashin.

 

Tashin farashin ya haifar da damuwa a tsakanin masu lura da watan Ramadan, wadanda ke dogaro da ‘ya’yan itatuwa don kula da lafiyarsu da kuzarin su a tsawon yini.

 

 

 

A halin da ake ciki, masana harkokin kiwon lafiya na ci gaba da jaddada muhimmancin ‘ya’yan itatuwa wajen kiyaye daidaiton abinci a cikin watan Ramadan.

 

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: ya yan itatuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Samar da makamashi mai tsafta na zamani shi ne fatanmu — Guterres

Babban Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, António Guterres,ya bayyana cewa, samar da makamashi mai tsabta da zai daidaita tsarin rayuwar dan Adam daga sarrafa wuta, ta hanyar yin amfani da tururi, zuwa rarrabuwar ma’adinan, shi ne ginshikin bunkasar al’umma.

Mista Gutterres ya bayyana hakan ne a taron inganta samar da makamshi da aka gudanar a harabar ofishin Majalisar Dinkin Duniya.

Ya ce “a yau, muna son tabbatar da yadda za a farka bisa tsarin sabon zamani. Rana tana fitowa don samar da makamashi mai tsabta ga al’umma.

A bara, kusan dukkanin sabbin qarfin wutar lantarki sun fito ne daga abubuwan da ake sabuntawa.

Zuba jari a harkar samar da makamashi mai tsafta darajarsa ta haura zuwa Dala tiriliyan 2 – Dala biliyan 800 fiye da abin da ake samu daga albarkatun mai.

Hasken rana da iska yanzu su ne hanyoyin samar da wutar lantarki mafi arha a duniya, kuma sassan makamashi masu inganci da suke samar da ayyukan yi, kuma suna kara habaka da ci gaba.

Kasashen da ke tattare da burbushin dake samar da makamashi ba sa iya kare tattalin arzikinsu, suna yi musu zagon kasa wanda ke haifar musu rasa wata babbar dama ta tattalin arziki a karni na 21.

Samar da tsabtataccen makamashi yana ba da damar ikon mallakar duk wani nau’i a fannin makamashi da tsaro.

Kasuwannin man fetur ya kasance daga cikin abubuwan yasa farashin da kuma gazawar samar da kayayyaki da rikice-rikice kamar yadda muka gani lokacin da Rasha ta mamaye Ukraine.

Amma sam duk da hauhawar farashin man fetur, farashin hasken rana, da bashi da takunkumin yana samar da iska, ga kusan kowace al’umma.

A karshe, tsabtataccen makamashi yana havaka, wanda hakan zai iya kai wa ɗaruruwan miliyoyin mutanen dake rayuwa ba tare da wutar lantarki ba a cikin sauri da araha, musamman ta hanyar dakile wutar lantarki da fasahar hasken rana.

Ana barin kasashe masu tasowa a baya. Har ila yau dai makamashin ya mamaye tsarin, kuma har yanzu hayakin yana karuwa lokacin da gaza aiki don gujewa faxawa rikicin sauyin yanayi. Don gyara wannan, muna buƙatar aiki domin daukar mataki.

Na farko, dole ne gwamnatoci su ba da himma wajen samar da tsaftataccen makamashi a nan gaba. A cikin watanni masu zuwa, kowace ƙasa ta yi alƙawarin gabatar da sabbin tsare-tsare na yanayi na ƙasa. Tare da manufa ta shekaru goma masu zuwa. Dole ne wadannan tsare-tsare su kasance sunyi daidaito tare da ƙayyadaddun yanayin zafi a duniya zuwa ma’aunin Celsius 1.5. Kasashen G20, wadanda ke da alhakin kusan kashi 80% na hayakin duniya, dole ne su jagoranci hakan.

Na biyu, dole ne mu gina tsarin makamashi na karni na 21. Ba tare da wata tangarda ta zamani ba, ƙarfin sabunta tsarin yanayi zai iya cika wannan buri namu. Amma ga kowace Dala da aka saka a cikin harkar wutar lantarki.

Na uku, dole ne gwamnatoci su kudiri aniyyar tabbatar da biyan buƙatun makamashi na duniya tare da sabuntawa. Dole ne manyan kamfanonin fasaha suma su taka rawarsu.

Zuwa shekarar 2030, cibiyoyin bayanai za su iya cinye wutar lantarki mai yawa kamar yadda Japan ke yi a yau. Kamfanoni ya kamata su himmatu wajen ba da iko tare da sabuntawa.

Na hudu, dole ne mu sanya adalci a cikin samar da canjin makamashi. Wannan yana nufin cewa tallafa wa al’ummomin da ke dogaro da albarkatun mai don shirya ingantaccen makamashi a nan gaba. Kuma yana nufin sake fasalin samar da ma’adanai mai muhimmanci.
Na biyar, dole ne mu tabbatar da an tsarin samar da makamashi.

Tsabtace hanyoyin samar da makamashi na da matuƙar tasiri wajen mayar da hankali sosai kuma kasuwancin duniya zai bunkasa.

Kasashen da suka kuduri aniyar samar da makamashi dole ne su yi aiki don rarraba kayayyaki, da rage haraji kan kayayyakin makamashi da kuma sabunta yarjejeniyar saka hannun jari ta yadda za su goyi bayan sauyin.

Na shida kuma na karshe, dole ne mu fitar da kudi zuwa ga qasashe masu tasowa. Afirka ta samu kashi biyu ne kacal na jarin da za a iya sabuntawa a bara, duk da cewa tana da kashi 60% na mafi kyawun albarkatun hasken rana a duniya.

Muna buƙatar matakan kasa da kasa don hana biyan basussuka da ake tsotsewa daga kasafin kudin wadannan ƙasashe masu tasowa da kuma ba da dama ga bankunan wajen ci gaban bunkasa ƙasashe da yawa su haɓaka ƙarfin ba da lamuni, da yin amfani da kuɗi masu zaman kansu sosai.

Muna kuma buƙatar hukumomin masu saka hannun jari da su yi la’akari da alƙawarin samar da makamashi mai tsafta.

Wani sabon yanayi na makamashi yana kusa da kai wa ga samun nasara, kuma zai zama da arha, sannan ya kasance wadataccen makamashi mai tsabta da zai samarwa duniya makamshi wadatacce, wajen bunkasa tattalin arziki, kasashe na ‘yancin cin gashin kai da kuma bayar da wutar lantarki kyauta ga kowa.

A nan lokacinmu ne da za mu iya ɗaukar nauyin sauyin duniya. Mu kuma yi amfani da shi yadda ya kamata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Samar da makamashi mai tsafta na zamani shi ne fatanmu — Guterres
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila
  • Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
  • An Kaddamar da Makon MNCH na 2025, Ya Rarraba Fakitin Bayarwa 6,000, Kayan C/S 500
  • Faransa Ta Bayyana Wuce Gona Da Irin ‘Yan Sahayoniyya Kan Falasdinawa Da Ayyukan Ta’addanci
  • Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati
  • An fara shigar da kayan agaji a Gaza