An yanke wa masu fyaɗe 3 hukuncin dandanƙewa da rataya a Kaduna
Published: 6th, March 2025 GMT
An yanke wa wasu mutum uku da aka kama da laifin fyaɗe hukuncin ratayewa da kuma dandaƙewa a Jihar Kaduna.
Kwamishinar Kula da Walwalar Jama”a, Hajiya Rabi Salisu, ta bayyana fatan cewa hukuncin da kotu ta yanke wa masu laifin zai zama darasi ga masu muguwar ɗabi’ar ta fyaɗe.
Da take sanar da hakan a ranar Laraba, kwamishinar ta bayyana cewa Ma’aikatar ta yi nasara a Shari’o’i uku da ta shigar da ƙara kan masu aikata fyaɗe a shekara gudanar ta gabata.
Ta bayyana cewa daga cikin mutanen akwai wanda Mai Shari’a Nana ta Babbar Kotun jihar ta yanke masa da hukuncin dandanƙewa da kuma kisa ta hanyar rataya, a watan Yuni shekarar 2024.
An kama korarren jami’in tsaro da ke sayar wa ’yan ta’adda makamai EFCC ta tsare tsohon Gwamnan Akwa Ibom kan almundahanar Naira biliyan 700 NAJERIYA A YAU: Me Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Su Ga Ragi A Farashin Man Fetur Ba?“Ranar 6 ga watan Fabrairu, 2025 kuma Mai Shari’a B. Yusuf na Babbar Kotun Jihar Kaduna ya yanke wa na biyun hukuncin dandanƙewa da kuma kisa ta hanyar rataya kan laifin fyaɗe.
“A ranar 24 ga watan kuma Mai Shari’a Isa Aliyu in yanke hukuncin ɗaurin rai-da-rai fa wanda wanda aka samu da laifin.”
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince Da Sabbin Kwamishinoni Biyu
Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da mutum biyu da Gwamna Uba Sani ya aike da sunayen su a tantance su a matsayin Kwamishinoni.
A cikin wata wasika da Gwamna Uba Sani ya aikawa Majalisar Dokokin, ya bukaci a amince da Farfesa Abubakar Sani Sambo a matsayin Kwamishinan Ilimin sai kuma Barrister Gloria Ibrahim a matsayin Kwamishinar Matasa da cigaban jihar.
Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, RT. Hon. Yusuf Dahiru Liman ya bukaci sabbin kwamishinonin da aka amince da su, su yi amfani da kwarewar su domin farfado da bangaren Ilimi da bunkasa ci gaban matasa.
Da yake ganawa da manema labarai jim kadan bayan tantancewa da amincewa da shi a matsayin Kwamishinan Ilimi, Farfesa Abubakar Sani Sambo ya lashi takobin gudanar da sauye-sauye a bangaren Ilimi ta hanyar fadada damarmaki, da yin garambawul a gine-gine da kuma inganta sha’anin koyarwa a makarantun dake fadin Jihar Kaduna.
Haka nan ita ma Barr. Gloria Ibrahim ta bayyana kudirinta na aiwatar da hangen nesa na Gwamna Uba Sani, na shigar da matasa cikin harkokin Mulki da ci gaba, sannan ta sha alwashin yin aiki tukuru wajen samar da damarmaki ga matasan dake fadin Jihar Kaduna.
Shamsuddeen Mannir Atiku