Aminiya:
2025-06-15@03:41:23 GMT

Wata mata ta kashe kishiyarta a Bauchi

Published: 5th, March 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Bauchi, ta fara bincike kan mutuwar wata mata mai shekaru 20, Hajara Isa, wadda aka tsinci gawarta a gidan mijinta aure.

Kakakin rundunar, Mohammed Ahmed Wakil, ya bayyana cewa sun samu rahoton rasuwar matar a ranar 3 ga watan Maris, 2025.

Ban taɓa cin zarafin Natasha ba, ina girmama mata — Akpabio EFCC ta tsare tsohon Gwamnan Akwa Ibom kan almundahanar Naira biliyan 700

Sai dai ya ce ’yan uwan mamaciyar suna zargi kishiyarta da hannu a mutuwarta.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Auwal Musa Muhammad, ya bayar da umarnin a gudanar da bincike domin gano gaskiyar lamarin.

Binciken farko ya kai ga kama kishiyar mamamciyar, mai suna Fatima Mohammed, mai shekaru 28.

Da aka tambaye ta, ta amsa cewar ta shaƙe Hajara har lahira, sannan ta zuba mata ruwan zafi da ƙone gawarta don ɓoye laifinta.

Rundunar ta bayyana cewa za a ci gaba da bincike a sashen binciken manyan laifuka na jihar (SCID).

Hakazalika, rundunar ta ce idan buƙatar tono gawar ta taso domin yin ƙarin bincike, za ta yi hakan don tabbatar da gaskiya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Kishiya

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi

Rundunar Ƴanandan Jihar Bauchi ta kama wani matashi mai suna Umar Yau, wanda aka fi sani da “Snake,” bisa zargin damfara ta yanar gizo da satar bayanan wasu mutane. An kama Yau, mai shekaru 25 daga unguwar Yelwan Makaranta a Bauchi, bayan binciken da aka fara sakamakon ƙorafi daga wata mata da ya damfara.

Fatimah Faiz Ali Bawahab, wata ’yar kasuwa ta yanar gizo, ta kai ƙorafin cewa wani ya ƙirƙiri asusun bogi a Facebook da sunanta da hotunanta don damfarar mutane. CSP Ahmed Wakil, kakakin rundunar, ya ce wanda ake zargin ya ƙirƙiri asusun “Amizeebaby Muhd” inda ya ke tallata kasuwancin ƙarya, yana karɓar kuɗi daga mutane ta asusun banki.

Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi Mataimakin Firaministan Sin Ya Gana Da Ministar Kudin Birtaniya

An gano cewa an taɓa damfarar wani Nafiu Muhd a watan Maris 2022, inda ya tura kudi zuwa asusun da ke dauke da suna Hansatu Yau, bayan haka aka toshe shi. Daga baya, bincike ya gano cewa ana amfani da sunayen Hansatu Yau da Umar Yau wajen karbar kuɗin jama’a a yanar gizo.

Bayan ƙorafin da aka samu, Kwamishinan ’Yansanda ya umurci gudanar da bincike na fasaha wanda ya kai ga kama Yau a ranar 5 ga Yuni, 2025. An kwato kati tara na ATM, katin zabe, na’urar MiFi, da sauran kayayyakin da suka tabbatar da laifin. Yau ya amsa cewa ya damfari mutane kusan 40 cikin shekaru biyar. An miƙa shi zuwa Rundunar ’Yansandan Kano don ci gaba da bincike da shari’a.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
  • An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato
  • Gobara Ta Ƙone Wani Gidan Mai A Legas
  • Gini ya kashe Ba’indiye a Zariya
  • Hajjin 2025: Jihohi 11 sun kashe N6.2bn wajen tallafa wa Alhazai