Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ya Raba Tallafin Ramadan A Mazabarsa
Published: 5th, March 2025 GMT
Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Yusuf Dahiru Liman, ya raba kayayyakin agaji na watan Ramadan na sama da Naira miliyan 200 ga al’ummar mazabarsa.
Ya yi hakan ne da nufin tallafa wa al’umma domin samun damar gudanar da azumin watan Ramadan cikin sauki, duba da halin da ake ciki na tabarbarewar tattalin arziki.
A wajen bikin kaddamar da rabon, Yusuf Dahiru Liman, wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatan ofishinsa, Bashir Adamu Nababa, ya jaddada aniyarsa ta rage wahalhalun da al’ummar mazabarsa ke fuskanta.
Ya bayyana rabon kayayyakin a matsayin wani bangare na alkawarin da ya dauka na inganta walwalar jama’a a yayin yakin neman zabe.
Shugaban kwamitin masu ruwa da tsaki, Isiyaku Adamu Nababa, ya jaddada cewa shirin ya nuna irin sadaukarwar da shugaban majalisar yake yi na yi wa al’ummarsa hidima baya ga ayyukan majalisa.
Ya bayyana sauran ayyukan jin kai da Yusuf Liman ya jagoranta, da suka hada da ayyuka a fannin ilimi, da kiwon lafiya, da kuma sanin makamar aiki.
Da yake jawabi a wajen taron, Hakimin Barnawa, Alhaji Kabiru Zubairu, ya bayyana jin dadinsa bisa jajircewar da kakakin majalisar ya yi wajen kyautata rayuwar al’ummar mazabarsa.
Ya yaba da yadda shugaban majalisar ke gudanar da jagoranci, wanda ke tafiya da kowa ba tare da bambancin addini ko kabila ba.
Shi ma mataimakin shugaban Karamar Hukumar Kaduna ta Kudu, Nehemiah Baba Karik, ya yaba da yadda Shugaban Majalisar yake aiki ba tare da nuna son kai ba, inda ya ce yana yi wa dukkan mazauna yankin hidima bisa adalci.
A nasa jawabin, Shugaban Majalisar Limamai da Malamai na mazabar Makera Malam Ibrahim Mahe, ya yaba da wannan karamci, inda ya ce ya zo a daidai lokacin da dace.
Ya kuma yi addu’ar Allah ya sakawa shugaban majalisar bisa kokarinsa na tallafawa al’ummar jihar Kaduna.
Wadanda suka ci gajiyar wannan karimcin sun hada da malamai maza da mata na makarantun islamiyya, da manyan limamai, da kungiyoyin Nisa’us Sunnah na Barnawa, da Makera, da Kakuri, da masu rike da sarautun gargajiya, da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC, da sauransu.
Sauran sun hada da hukumomin tsaro da suka hada da rundunar sa kai ta Civilian JTF, da kuma kungiyoyin agaji na JIBWIS, da Fityanul Islam, da Jama’atu Nasril Islam da dai sauransu.
Da dama daga cikin wadanda suka ci gajiyar shirin sun nuna matukar godiya ga wannan karamcin, inda suka yi addu’o’in Allah ya ci gaba da yi ma shugaban majalisar jagoranci da samun nasara a ayyukansa.
Shamsuddeen Mannir Atiku
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Tallafin Ramadan Shugaban Majalisar shugaban majalisar
এছাড়াও পড়ুন:
ZAMFARA: APC Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Dauki Don Matsalar Tsaro Na Kara Tsananta
Jam’iyyar APC reshen jihar Zamfara, ta bayyana matukar damuwarta kan yadda matsalar tsaro ke kara ta’azzara a jihar, inda ta bayyana hakan a matsayin abin ban tsoro da rashin fahimta.
A wata sanarwa dauke da sa hannun sakataren yada labarai na jam’iyyar, Yusuf Idris Gusau, jam’iyyar APC ta ce yawaitar ‘yan fashi da makami, garkuwa da mutane da kashe-kashe a Zamfara ya kai matakin da ba a taba ganin irinsa ba, yayin da ta zargi gwamnatin jihar a karkashin Gwamna Dauda Lawal da nuna halin ko in kula.
A cewar sanarwar, jam’iyyar ta damu matuka da wani faifan bidiyo na baya-bayan nan inda aka ga sama da mutane 200 mazauna Kaura Namoda suna rokon a taimaka musu biyo bayan sace su da wasu da ake zargin ‘yan fashi ne suka yi.
Jam’iyyar APC ta kuma soki gwamnatin kan abin da ta bayyana a matsayin rashin mayar da martani da kuma rashin cika alkawarin da ta dauka na kare rayuka da dukiyoyi a lokacin yakin neman zabe.
Jam’iyyar ta tuna cewa, Gwamna Dauda Lawal ya yi kakkausar suka ga gwamnatocin baya kan rashin tsaro, ya kuma yi alkawarin kawo karshen ‘yan fashi a cikin watanni biyun farko na mulki.
Sai dai jam’iyyar APC ta bayyana cewa a maimakon haka lamarin ya tabarbare, inda a kullum ake ta yin garkuwa da mutane da kashe-kashe a sassan jihar.
Sanarwar ta kuma bayyana wasu muhimman hanyoyi da suka hada da Gusau –Talata Mafara –Tureta, da Mayanchi –Anka –Gummi – wadanda a yanzu suke da hatsarin tafiya ba tare da rakiyar sojoji ba.
Jam’iyyar ta kara da cewa, hanyar Gusau zuwa Kaura Namoda ta zama daya daga cikin mafi hadari, inda a kullum ake samun rahotannin sace-sacen mutane da kashe-kashe.
Da take ba da misalin harin baya-bayan nan da aka ce an kashe mutane 38 da aka yi garkuwa da su daga unguwar Banga da ke karamar hukumar Kaura Namoda bayan an biya kudin fansa, jam’iyyar APC ta ce gwamnatin jihar ta yi shiru duk da cewa ana ci gaba da samun tashin hankali a tsakanin mazauna yankin.
A yayin da wasu sabbin rahotanni suka ce an sace sama da mutane 200 a cikin makon nan, jam’iyyar APC ta sake yin kira ga gwamnatin tarayya da ta kafa dokar ta-baci a Zamfara domin ba da damar aikewa da karin sojoji da kuma aiwatar da sahihin matakan tsaro.
Jam’iyyar ta zargi gwamnatin jihar da gazawa yadda ya kamata ga hukumomin tsaro na tarayya tare da zargin gwamnan da wasu mataimakansa kan harkokin yada labarai sun fito fili suna sukar ayyukan sojoji a jihar.
“Haka zalika ta yi Allah-wadai da rufe kasuwanni da hana zirga-zirgar ababen hawa, inda ta bayyana su a matsayin matakan da ba su da inganci da suka yi illa ga tattalin arzikin jihar.
Jam’iyyar APC ta kuma yi kakkausar suka kan tafiye-tafiyen da Gwamna Lawal ya yi a kasashen waje, inda ta yi zargin cewa yana halartar bukukuwan ‘yan uwa na kashin kansa yayin da mazauna gida ke kokawa da rashin tsaro.
Jam’iyyar ta yabawa bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara karkashin jagorancin Bashar Aliyu Gummi bisa jajircewar da ta yi wajen ganin ta yi wa bangaren zartarwa hukunci kan al’amuran da suka shafi rashin tsaro da cin hanci da rashawa.
A karshe jam’iyyar APC ta jajantawa iyalan wadanda rikicin ya shafa tare da yin addu’ar Allah ya dawo mana da zaman lafiya a jihar Zamfara da Najeriya baki daya.
REL/AMINU DALHATU