Ban taɓa cin zarafin Natasha ba, ina girmama mata — Akpabio
Published: 5th, March 2025 GMT
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya nesanta kansa daga zargin cin zarafin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, inda ya ce mahaifiyarsa ta ba shi tarbiyya mai kyau, kuma yana mutunta mata.
Akpabio ya bayyana hakan ne bayan da Sanata Natasha ta zarge shi da cin zarafinta ta hanyar neman kwanciya da ita, wanda ya haifar da rikici a zauren majalisa.
A cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce: “Ina son duniya ta sani cewa ban taba cin zarafin Sanata Natasha ko wata mace ba. Mahaifiyata ta yi min tarbiyya mai kyau, ina girmama mata.”
Wannan bayani na Akpabio ya zo ne a yayin da ake ta cece-kuce kan rikicinsa da Sanata Natasha, wanda ya samo asali daga zargin da ta yi masa kan wasu abubuwa da suka faru a baya.
Rikicin ya ɗauki sabon salo a zauren majalisar bayan da aka buƙaci ta sauya wajen zama, wanda ta ƙi amincewa da shi.
A zaman majalisar na baya, Sanata Natasha ta tsaya kai da fata tana kare kanta, inda ta nuna rashin amincewarta da matsin lamba da ta ke fuskanta.
Wannan ya jawo ruɗani a majalisar har aka buƙaci jami’an tsaro su fitar da ita daga zauren.
Sai dai, a cikin bayaninsa, Akpabio ya ce ba ya gaba da Sanata Natasha, kuma yana girmama mata a kowane hali.
Ya ce: “Tun daga yarinta, an koya min daraja mata, kuma a matsayina na jagora, ba zan taɓa nuna wariya ko cin zarafi ga kowace mace ba.”
A yanzu, jama’a na ci gaba da bibiyar wannan rikici don ganin yadda za a warware shi, yayin da ‘yan majalisa ke ƙoƙarin shawo kan lamarin domin kada rikicin ya ƙara ta’azzara a cikin majalisar dattawa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: cin zarafi Majalisar Dattawa Ruaɗani zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Kwamitin Neman Sabuwar Karamar Hukumar Kanya Babba Ya Gabatar Da Takardar Bukatarsa Ga Majalisar Dattawa
Kwamitin neman sabuwar Karamar Hukumar Kanya Babba daga Karamar Hukumar Babura ta Jihar Jigawa, ya gabatar da takardar bukatarsa ga kwamitin Majalisar Dattawa mai kula da kirkiro jihohi da kananan hukumomi a zaman da aka yi a jihar Kano.
A yayin mika takardar, Shugaban kwamitin kuma Hakimin Kanya Babba, Makaman Ringim, Malam Mohammed Ibrahim ya bayyana cewar wannan yunkuri ya bi duk sharuddan da kundin tsarin mulki ya shimfida don kafa sabuwar karamar hukuma.
Makaman na Ringim ya kara da cewar, daukacin al’ummar yankin Kanya Babba, ciki da wajen mazabar na matukar goyon bayan hakan domin bunkasa ci gaban tattalin arziki da al’umma a yankin.
Da yake karbar takardar, Shugaban kwamitin Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibril, ya nuna jin dadin sa da jajircewar mutanen Kanya Babba wajen mika takardar.
Barau Jibrin, ya kuma tabbatar musu kwamitinsa zai yi adalci da gaskiya a aikin da aka dora musa.
Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, taron mika bukatar ya samu halartar mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Injiniya Aminu Usman da Sanatan Jigawa ta Arewa maso Yamma, Alhaji Babangida Husaini da dan majalisar jiha mai wakiltar mazabar Kanya, Alhaji Ibrahim Hashim Kanya da shugaban Karamar Hukumar Babura, Alhaji Hamisu Muhammad Garu da mai bawa gwamna shawara kan harkokin bada aiyukan kwangila Usman Haladu Isa da Alhaji Salisu Muazu Kanya da hakimai da Dagatai da ‘yan siyasa da kuma sauran masu ruwa da tsaki da dimbin masoya.
Usman Mohammed Zaria