Ban taɓa cin zarafin Natasha ba, ina girmama mata — Akpabio
Published: 5th, March 2025 GMT
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya nesanta kansa daga zargin cin zarafin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, inda ya ce mahaifiyarsa ta ba shi tarbiyya mai kyau, kuma yana mutunta mata.
Akpabio ya bayyana hakan ne bayan da Sanata Natasha ta zarge shi da cin zarafinta ta hanyar neman kwanciya da ita, wanda ya haifar da rikici a zauren majalisa.
A cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce: “Ina son duniya ta sani cewa ban taba cin zarafin Sanata Natasha ko wata mace ba. Mahaifiyata ta yi min tarbiyya mai kyau, ina girmama mata.”
Wannan bayani na Akpabio ya zo ne a yayin da ake ta cece-kuce kan rikicinsa da Sanata Natasha, wanda ya samo asali daga zargin da ta yi masa kan wasu abubuwa da suka faru a baya.
Rikicin ya ɗauki sabon salo a zauren majalisar bayan da aka buƙaci ta sauya wajen zama, wanda ta ƙi amincewa da shi.
A zaman majalisar na baya, Sanata Natasha ta tsaya kai da fata tana kare kanta, inda ta nuna rashin amincewarta da matsin lamba da ta ke fuskanta.
Wannan ya jawo ruɗani a majalisar har aka buƙaci jami’an tsaro su fitar da ita daga zauren.
Sai dai, a cikin bayaninsa, Akpabio ya ce ba ya gaba da Sanata Natasha, kuma yana girmama mata a kowane hali.
Ya ce: “Tun daga yarinta, an koya min daraja mata, kuma a matsayina na jagora, ba zan taɓa nuna wariya ko cin zarafi ga kowace mace ba.”
A yanzu, jama’a na ci gaba da bibiyar wannan rikici don ganin yadda za a warware shi, yayin da ‘yan majalisa ke ƙoƙarin shawo kan lamarin domin kada rikicin ya ƙara ta’azzara a cikin majalisar dattawa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: cin zarafi Majalisar Dattawa Ruaɗani zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
Duk da cewa, yanayin zafi ya yawaita a kasar ta Saudiyya, yayin gudanar da aikin Hajjin 2025, koda-yake; akasarin wadanda suka mutu daga Nijeriyar tsofaffi ne.
Rasuwar farko da aka sanar ta wani Alhaji ce daga Jihar Oyo, Alhaji Sulaimon Hamzat, wanda ya rasu a ranar 17 ga Mayun 2025 a kasar ta Saudiyya.
Na biye da shi kuma daga Jihar Abiya ne, mai suna Alhaji Saleh, Shugaban Kasuwar Shanu ta Lokpanta, wanda ya rasu a garin Makka a daren ranar Litinin 26 ga watan Mayun 2025.
Bayan haka kuma, sai wata Hajiya mai shekaru 75 daga Jattu Uzairue a Karamar Hukumar Etsako ta yamma da ke Jihar Edo, Adizatu Dazumi, wadda ta mutu a ranar Litinin 26 ga Mayun 2025, bayan gajeriyar rashin lafiya.
An samu rahoton cewa, Dazumi ta kamu da rashin lafiya jim kadan bayan kammala dawafi, inda aka garzaya ta ita zuwa asibitin Sarki Fahad da ke Makka a ranar Lahadi, washegari kuma ta mutu.
Haka zalika, wata Hajiya daga Jihar Filato ta rasu a birnin Makka da ke Saudiyya, yayin gudanar da wannan aiki Hajjin 2025.
Marigayiyar, mai suna Hajiya Jamila Muhammad, ta rasu ne sakamakon cutar Siga da ke fama da shi a asibitin Sarki Abdul’aziz da ke birnin Makka.
Kwana daya kafin fara aikin Hajjin 2025, wani Alhaji daga Jihar Kano mai suna Shu’aibu Jibrin, ya rasu a garin Makka.
Haka nan kuma, wani Alhajin Nijeriya ya rasu a filin Arfa.
A cewar Shugaban Hukumar Alhazai ta Nijeriya, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, “Mun samu labari mara dadi cewa; mun rasa mahajjatanmu a yau Arfat, dayan kuma ya rasu kafin mu bar Makka,” in ji shi.
Ya kuma ce, mutuwar Alhazan daga Allah ne; inda ya kawar da rade-radin da ake yin a cewa, zafin rana ne ya haddasa su.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp