Sin Na Matukar Adawa Da Manufar Kariyar Ciniki Da Babakeren Amurka
Published: 5th, March 2025 GMT
Tun ranar 4 ga watan nan da muke ciki, Amurka ta fake da batun maganin Fentanyl, da nufin kakabawa Sin karin harajin kwastam na kashi 10% kan kayayyakin kirar kasar Sin da za ta shigar da su kasar Amurka. Game da wannan mummunan mataki mai sabawa ka’idar cinikin duniya da karya lagon tsarin kasuwanci tsakanin kasashen biyu, ba shakka Sin na matukar adawa da shi, kuma ba za ta zura ido ta rungume hannu tana ta kallo kawai ba.
To, saboda ganin Amurka tana son nacewa kan batun maganin Fentanyl, ya zama wajibi mu san gaskiya game da batun. Jiya Talata 4 ga watan nan da muke ciki, gwamnatin Sin ta gabatar da takardar bayani kan matakan kayyade maganin Fentanyl ta Sin, inda Sin ta yi bayani kan dimbin ayyuka da take gudanarwa da amfani da fasaha da dabarun da take da shi na kayyade amfani da wannan magani a kasar. Muna iya fahimta daga takardar cewa, Sin daya ce daga cikin kasashen duniya mafi tsauraran manufofi na dakile miyagun kwayoyi da nuna iyakacin kokarin kawar da wannan mummunan aiki tun daga tushe a kasar. A shekarun nan baya, Sin ta amince da matakan da Amurka ke dauka kan batun Fentanyl bisa tunanin jin kai, amma sabanin da fahimtar da Sin take nuna mata, Amurka tana fakewa da wannan batu da nufin matsa mata lamba a bangaren harajin kwastam.
Amurka ba za ta magance matsalar Fentanyl dake dabaibaye kasar ba, sai ta yi shawarwari da bangaren Sin, don daidaita abubuwan dake tsakaninsu. Sin za ta bude kofarta don rungumar shawarwari tsakaninsu, amma idan Amurka tana nufin cimma wata boyayyiyar manufarta ta hanyar yakin harajin kwastam, to Sin za ta mayar da tsattsauran martani ba tare da bata lokaci ba. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: harajin kwastam
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Sa’o’ii 72
Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Bangaren Guda kuma na sa’o’ii 72 ko kwanaki 3, daga 8-10 na watan Mayu mai zuwa.
Jaridar Daily Trust ta Najeriya nakalto jakadan kasar Rasha a Abuja yana fadar haka a wani taro baje kolin hotinan yaki Rasah da Nazi a dai dai lokacinda kasar take cikar shekaru 80 da samun nasara a kan sojojin Nazi a karshen yakin duniya na II a Abuja.
Andrey Podelyshev yace idan kasar Ukraine ta zami da tsagaita wuta a cikin wadannan kwanaki ba laifi, amma kuma idan sojojinta sun kai wani hari a kan rasha ta zata rama da hare-hare masu tsanani.
Shugaban Volodimir Zelesky dai tuni ya yi watsi da tsagaita wutar ya kura kara da cewa Rasha tana son ta ja hankalin duniya ne da wannan tsagaita wuta, don amfanin kanta a yakin da suke fafatawa. A halin yanzu dai an dai kwanaki kimani 1,159 aka fafatawa tsakanin kasashen biyu.