Tun ranar 4 ga watan nan da muke ciki, Amurka ta fake da batun maganin Fentanyl, da nufin kakabawa Sin karin harajin kwastam na kashi 10% kan kayayyakin kirar kasar Sin da za ta shigar da su kasar Amurka. Game da wannan mummunan mataki mai sabawa ka’idar cinikin duniya da karya lagon tsarin kasuwanci tsakanin kasashen biyu, ba shakka Sin na matukar adawa da shi, kuma ba za ta zura ido ta rungume hannu tana ta kallo kawai ba.

A wannan ranar kuwa, Sin ta mayar da martani, inda da farko ta kai kara a gaban kunigyar cinikin duniya ta WTO kan matakin da Amurka ke dauka, daga baya ta kara kakabawa Amurka harajin kwastam kan wasu kayayyakin da za a shigo da su kasarta, har ma ta shigar da wasu kamfanoni masu ruwa da tsaki cikin jerin sunaye wadanda ba su da aminci a kasar Sin. Jerin matakan da Sin take dauka na mayar da martani sun bayyana niyyar Sin ta kare halastaciyyar moriyarta da kiyaye tsarin cinikin duniya tsakanin mabambantan bangarori, abin da ya zama wajibi kuma ya dace da halin da ake ciki.

To, saboda ganin Amurka tana son nacewa kan batun maganin Fentanyl, ya zama wajibi mu san gaskiya game da batun. Jiya Talata 4 ga watan nan da muke ciki, gwamnatin Sin ta gabatar da takardar bayani kan matakan kayyade maganin Fentanyl ta Sin, inda Sin ta yi bayani kan dimbin ayyuka da take gudanarwa da amfani da fasaha da dabarun da take da shi na kayyade amfani da wannan magani a kasar. Muna iya fahimta daga takardar cewa, Sin daya ce daga cikin kasashen duniya mafi tsauraran manufofi na dakile miyagun kwayoyi da nuna iyakacin kokarin kawar da wannan mummunan aiki tun daga tushe a kasar. A shekarun nan baya, Sin ta amince da matakan da Amurka ke dauka kan batun Fentanyl bisa tunanin jin kai, amma sabanin da fahimtar da Sin take nuna mata, Amurka tana fakewa da wannan batu da nufin matsa mata lamba a bangaren harajin kwastam.

Amurka ba za ta magance matsalar Fentanyl dake dabaibaye kasar ba, sai ta yi shawarwari da bangaren Sin, don daidaita abubuwan dake tsakaninsu. Sin za ta bude kofarta don rungumar shawarwari tsakaninsu, amma idan Amurka tana nufin cimma wata boyayyiyar manufarta ta hanyar yakin harajin kwastam, to Sin za ta mayar da tsattsauran martani ba tare da bata lokaci ba. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: harajin kwastam

এছাড়াও পড়ুন:

Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba

Kungiyar cinikayya ta duniya wato WTO, ta gudanar da taron shekara-shekara na biyu, na hukumar zartaswar cinikayyar hidimomi a birnin Geneva dake kasar Switzerland a jiya Juma’a, inda bangaren Sin ya yi nuni da cewa, matakin Amurka game da harajin kwastam na tattare da rashin fahimta da rashin gaskiya a wasu fannoni, don haka ya bukaci bangaren Amurka da ta bi ka’idojin kungiyar WTO, da daidaita matsaloli ta hanyar yin hadin gwiwa a tsakanin bangarori daban daban, da dakatar da daukar matakai daga bangare daya, don tabbatar da tsarin ciniki na duniya tare da bangarori daban daban. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba
  • Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
  • Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Afirka Sun Yi Alkawarin Karfafa Alaka
  • MDD: Adadin ‘Yan Gudun Hijira A Duniya Ya Kai Miliyan 122