Leadership News Hausa:
2025-11-03@09:56:29 GMT

An Bude Taron Shekara-shekara Na Majalisar Dokokin Kasar Sin

Published: 5th, March 2025 GMT

An Bude Taron Shekara-shekara Na Majalisar Dokokin Kasar Sin

A cewar rahoton, za a samar tare da aiwatar da wani tsari mai wa’adin shekaru 3, wanda zai mayar da hankali wajen karfafa bangaren ilimi.

Haka kuma, kasar za ta inganta raya ilimin dole mai inganci kuma bisa daidaito, tare da kara bayar da damar shiga makarantun sakandare.

Rahoton ya kuma bayyana cewa, kasar Sin za ta inganta hada ilimin sana’o’i da ilimi na gama gari, tare da hada hannu da masana’antu da makarantu ta yadda ilimin sana’o’i zai kara dacewa da tsarin ilimi.

Rahoton ya kara da cewa, kasar Sin za ta aiwatar da gyare-gyare a makarantun gaba da sakandare cikin rukunoni, tare da daukar matakai masu kwari wajen fadada ingancin karatu da gaggauta samar da jami’o’i da bangarorin kwarewa da za su kai matsayi mafi kyau a duniya.

Kasar Sin ta ce, tana adawa da duk wani nau’i na kariyar cinikayya da zartar da ra’ayi na kashin kai, kuma za ta daukaka tabbatar da adalci da daidaito a duniya.

Rahoton ya kara da cewa, kasar za ta ci gaba da nacewa ga manufar diplomasiyya mai zaman kanta da bin tafarkin neman ci gaba cikin lumana.

A cewar rahoton, a shirye kasar Sin take ta hada hannu da sauran kasashen duniya wajen samar da duniya mai adalci da rabuwar iko tsakanin kasa da kasa da dunkule tattalin arzikin duniya, ta yadda kowa zai amfana da ita da inganta aiwatar da shawarar ci gaban duniya da ta samar da tsaro a duniya da ta wayewar kan al’ummun duniya. Haka kuma, za ta shiga a dama da ita wajen aiwatar da gyare-gyare a tsarin tafiyar da harkokin duniya da yayata shawarar gina al’umma mai makoma ta bai daya ga dukkan bil Adama da kuma samar da makomar zaman lafiya da ci gaba ga duniya.

Bugu da kari, rahoton ya ce, Sin za ta daukaka burinta na ganin dunkulewar kasar, inda ya ce, za ta inganta cibiyoyi da manufofin raya tattalin arziki da musayar al’adu da hadin kai a fadin mashigin Taiwan da fadada ayyukan raya gabobi 2 na mashigin, ta yadda za a kyautata walwalar daukacin Sinawa na gabobin 2 na mashigin Taiwan na kasar Sin.

Rahoton ya nuna cewa, kasar za ta zurfafa hade dabarun raya masana’antu masu tasowa bisa manyan tsare-tsare da sauran dimbin kokarin karfafa ci gaban wadanda za a kafa nan gaba.

Rahoton aikin ya ce, kasar Sin za ta aiwatar da shirye-shiryen nuna yadda za a yi amfani da manyan sabbin fasahohi, da kayayyaki da tsare-tsaren ciyar da al’amura gaba, da matsa kaimi ga bunkasa harkokin kasuwanci cikin aminci da inganci, da tattalin arzikin kananan jirage masu tashi kasa-kasa, da sauran masana’antu masu tasowa.

Har ila yau, rahoton ya ce, kasar za ta bullo da hanyar da za ta kara samar da kudade ga masana’antun da za a kafa nan gaba da kuma karfafa ci gaban masana’antu kamar na sarrafa halittu, da fasahar daidaita makamashi ta ‘quantum’, da fasahar kere-keren kirkirarriyar basira AI, da kuma fasahar sadarwa ta 6G.

A cewar rahoton, kasar Sin za ta ba da goyon baya ga bunkasa kanana da matsakaitan kamfanoni masu zaman kansu a shekarar 2025, inda ya kara da cewa, kasar za ta ci gaba da zurfafa raya sana’o’in kirkire-kirkire, da inganta ci gaban kanana da matsakaitan masana’antu da ke amfani da fasahohin zamani na musamman domin samar da sabbin kayayyaki da za su kasance daban da na saura.

 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kasar Sin za ta kasar za ta

এছাড়াও পড়ুন:

Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa za ta ci gaba da shirin gudanar da babban taronta wanda za a yi a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba a Ibadan da ke Jihar Oyo.

Tun da farko, Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta hana jam’iyyar gudanar da taron, inda ta ce PDP ta karya dokokinta na cikin gida.

’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi Kotu ta dakatar da gudanar da babban taron PDP

Mai shari’a James Omotosho, wanda ya jagoranci shari’ar, ya umarci Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), da kada ta karɓi ko ta wallafa sakamakon taron har sai PDP ta cika dukkanin sharuɗan da doka ta tanada.

Sai dai a cikin wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar da yammacin ranar Juma’a, kakakinta na ƙasa, Debo Ologunagba, ya ce jam’iyyar ba za ta dakatar da shirin gudanar da taron ba.

Ya bayyana hukuncin kotun a matsayin tauye haƙƙin dimokuraɗiyya a Najeriya.

Ologunagba, ya ce hukuncin ba zai hana PDP ci gaba da shirye-shiryenta na zaɓen sabbin shugabanni da za su jagoranci jam’iyyar na tsawon shekaru huɗu masu zuwa ba.

Ya yi nuni da cewa Kotun Ƙoli ta tabbatar da cewa jam’iyyu na da ’yancin tafiyar da harkokinsu na cikin gida.

“PDP na kira ga mambobinta da shugabanni a faɗin ƙasar nan da su kuma ci gaba da shirye-shiryen babban taron jam’iyyar,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa jam’iyyar mai bin doka ce, kuma ta umarci lauyoyinta da su ɗaukaka ƙara game da hukuncin kotun.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu
  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa