MDD Ta Nuna Cikakken Goyon Bayanta Ga Shirin Sake Gina Gaza Da Larabawa Su Ka Gabatar
Published: 5th, March 2025 GMT
Babban magatakardar MDD Antonio Guterres wanda ya halarci taron da kasashen larabawa suke yi a Masar, ya bayyana goyon bayansa ga tsarin da su ka bijiro da shi na sake gina yankin Gaza, ba tare da an fitar da Falasdinawa daga cikinsa ba.
Gutress ya ce; Ina maraba da kuma nuna cikakken goyon bayana ga shirin da taron kungiyar kasashen larabawa ta bijiro da shi na sake gina Gaza.
Gutrress ya kuma ce: MDD a shirye take ta shiga da karfi a yi wannan aikin da ita.
Haka nan kuma babban magatakardar MDD ya yi kira da a dauki duk matakin da ya kamata domin ganin ba a sake komawa yaki a Gaza ba.
Gutteres ya kuma ce, Gaza ba ta da makoma wacce ta wuce ta kasance a karkashin daular Falasdinawa.
Babban magatakardar MDD ya bayyana taron na kasashen larabawa da cewa yana da matukar muhimmanci domin daukar nauyi a jumlace da zai kai ga kawo karshen yakin Gaza.
A jiya Talata ne dai kasashen larabawa su ka hadu a Alkahira ta kasar Masar domin halartar taron tattauna hanyoyin sake gina Gaza da kuma kalubalantar manufar Amurka da HKI na korar Falasdinawa daga Gaza.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasashen larabawa
এছাড়াও পড়ুন:
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
Ya kuma bayyana cewa kasar Sin wuri ne mai kyau ga harkokin zuba jari ga ‘yan kasuwa na duniya. Ya ce hadin gwiwa da kasar Sin yana nufin hadin gwiwa da damammaki, imani da kasar Sin yana nufin imani da kyakkyawar makoma, zuba jari a kasar Sin yana nufin zuba jari mai riba ta dogon zango.(Safiyah Ma)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA