Rundunar ’yan sandan Nijeriya ta sanar da cewa a ɗakin wani otel ta gano gawar wani tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Ficen Nijeriya, David Shikfu Parradang.

A baya dai an ruwaito cewa wasu masu garkuwa da mutane ne suka kashe Mista Parradang bayan sun karɓe kuɗin da ya ciro a banki a yankin Area 1 da ke babban birnin ƙasar.

Masu garkuwa sun kashe tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Fice a Abuja Tinubu ya naɗa Babatunde Ogunjimi Akanta Janar na Tarayya

Sai dai wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Abuja, Josephine Adeh ta fitar a yammacin wannan Talatar, ta ce tsohon babban jami’in Hukumar Shige da Ficen ya mutu ne a ɗakin wani otel saɓanin rahoton da ke cewa masu garkuwa da mutane ne suka kashe shi.

Adeh ta ce rasuwar Mista Parradang na zuwa ne bayan ya yi wata baƙuwa mace da ta kai masa ziyara ɗakin otel ɗin ya kama na kwana guda.

“Bisa rahotanni da ke cewa an yi garkuwa da tsohon jami’in Hukumar Shige da Ficen sannan daga bisani aka kashe, muna so mu tabbatar da gaskiyar lamarin.

“Abin da ya faru shi ne da misalin ƙarfe 12 na ranar 3 ga watan Maris, Mista Parradang ya ziyarci Otel ɗin Joy House da ke yankin Area 3 na Abuja a wata baƙar mota ƙirar marsandi.

“Ya biya Naira 22,000 kuɗin kwana ɗaya. Sai dai bayan wani ɗan lokaci ya buƙaci ɗaya daga cikin masu aiki a otel ɗin cewa ya yi baƙuwa yana so a rako ta ɗakin nasa.

“Matar da ta kai masa ziyara ta bar otel ɗin da misalin ƙarfe 4 na yammacin wannan rana.

“Har bayan tafiyar wannan mata Mista Parradang bai fito daga ɗakin ba, sai washegari da misalin ƙarfe 4 na asubahi wani abokinsa mai aikin ɗamara ya biyo sawu yana cigiyarsa har otel ɗin.

“Yana zuwa kuwa aka garzaya da shi [abokin nasa] har ɗakin, inda aka tarar da gawarsa zaune a kan kujera.

“Nan da nan aka sanar da ofishin ’yan sanda na Durumi kuma suka zo suka ɗauki hotuna da sauraren ababen da su taimaka musu wajen gudanar da bincike.”

Sanarwar ta ƙara da cewa, a halin yanzu an miƙa gawar Mista Parradang zuwa Asibitin Ƙasa da ke Abuja domin ɗauka matakan da suka dace “yayin da ma’aikatan otel ɗin ke ci gaba da bai wa ’yan sanda haɗin kai a binciken da suka gudanarwa.”

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: David Shikfu Parradang Hukumar Shige da Fice Hukumar Shige da Mista Parradang

এছাড়াও পড়ুন:

Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno

Wasu abubuwan fashewa da ake zargin ’yan ta’addan Boko Haram ne suka dasa, sun kashe kimanin mutane 26, ciki har da mata da ƙananan yara a kusa da garin Rann da ke Ƙaramar Hukumar Kala Balge ta Jihar Borno.

Majiyoyin tsaro da na cikin gari sun bayyana cewa mutane da dama sun jikkata bayan da motar da ke ɗauke da wadanda abin ya shafa zuwa Gambarou Ngala ta taka abin fashewar.

Wata majiya ta ce, “Ba a tantance adadin mutanen da suka mutu ba, amma rahotanni na farko sun nuna cewa mata huɗu da yara shida da maza 16 ne suka mutu a wannan fashewar.”

Ta ci gaba da cewa lamarin ya faru ne a kan hanyar Furunduma, kimanin kilomita 11 daga garin Rann, da misalin karfe 11 na safe a ranar Litinin.

Mutanen da talauci ya yi wa katutu zai ƙaru a Nijeriya — Bankin Duniya NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya

Ta ƙara da cewa an kai wasu da suka jikkata asibitin Rann domin kula da su.

Babu wata sanarwa a hukumance daga bangaren sojoji ko ’yan sanda game da faruwar lamarin.

Sai dai kuma, kokarin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Borno, Kenneth Daso, bai yiwu ba saboda layin wayarsa ba ya shiga.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji kuskure ne — Janar Chibuisi