‘A ɗakin otel muka tsinci gawar tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Fice’
Published: 4th, March 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Nijeriya ta sanar da cewa a ɗakin wani otel ta gano gawar wani tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Ficen Nijeriya, David Shikfu Parradang.
A baya dai an ruwaito cewa wasu masu garkuwa da mutane ne suka kashe Mista Parradang bayan sun karɓe kuɗin da ya ciro a banki a yankin Area 1 da ke babban birnin ƙasar.
Sai dai wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Abuja, Josephine Adeh ta fitar a yammacin wannan Talatar, ta ce tsohon babban jami’in Hukumar Shige da Ficen ya mutu ne a ɗakin wani otel saɓanin rahoton da ke cewa masu garkuwa da mutane ne suka kashe shi.
Adeh ta ce rasuwar Mista Parradang na zuwa ne bayan ya yi wata baƙuwa mace da ta kai masa ziyara ɗakin otel ɗin ya kama na kwana guda.
“Bisa rahotanni da ke cewa an yi garkuwa da tsohon jami’in Hukumar Shige da Ficen sannan daga bisani aka kashe, muna so mu tabbatar da gaskiyar lamarin.
“Abin da ya faru shi ne da misalin ƙarfe 12 na ranar 3 ga watan Maris, Mista Parradang ya ziyarci Otel ɗin Joy House da ke yankin Area 3 na Abuja a wata baƙar mota ƙirar marsandi.
“Ya biya Naira 22,000 kuɗin kwana ɗaya. Sai dai bayan wani ɗan lokaci ya buƙaci ɗaya daga cikin masu aiki a otel ɗin cewa ya yi baƙuwa yana so a rako ta ɗakin nasa.
“Matar da ta kai masa ziyara ta bar otel ɗin da misalin ƙarfe 4 na yammacin wannan rana.
“Har bayan tafiyar wannan mata Mista Parradang bai fito daga ɗakin ba, sai washegari da misalin ƙarfe 4 na asubahi wani abokinsa mai aikin ɗamara ya biyo sawu yana cigiyarsa har otel ɗin.
“Yana zuwa kuwa aka garzaya da shi [abokin nasa] har ɗakin, inda aka tarar da gawarsa zaune a kan kujera.
“Nan da nan aka sanar da ofishin ’yan sanda na Durumi kuma suka zo suka ɗauki hotuna da sauraren ababen da su taimaka musu wajen gudanar da bincike.”
Sanarwar ta ƙara da cewa, a halin yanzu an miƙa gawar Mista Parradang zuwa Asibitin Ƙasa da ke Abuja domin ɗauka matakan da suka dace “yayin da ma’aikatan otel ɗin ke ci gaba da bai wa ’yan sanda haɗin kai a binciken da suka gudanarwa.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: David Shikfu Parradang Hukumar Shige da Fice Hukumar Shige da Mista Parradang
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida
Kungiyar Kare Hakkokin Dan Adam ta Siriya ta bayyana sabbin mutanen da suka mutu sakamakon harin Suweida
Kungiyar kare hakkin dan adam ta Siriya (SOHR) ta bayyana wasu sabbin fararen hula tara da aka ci zarafinsu a lokacin abubuwan da suka faru a Suweida a watan Yulin da ya gabata.
Hukumar da ke sa ido kan lamarin ta bayyana cewa, wadanda aka kashen da suka hada da mata biyu, an kashe su ne a filin wasa a lokacin da wasu ma’aikatun tsaro da na cikin gida na gwamnatin rikon kwarya suke lardin na Suweida, tare da halartar mayakan ‘yan kabilar Larabawan Bedouin.
Hukumar da ke sa ido kan lamarin ta ce adadin mutanen da suka mutu a watan Yulin da ya gabata a tsakanin al’ummar Druze a Suweida ya kai 1,592, yayin da adadin wadanda suka mutu tun safiyar Lahadi 13 ga watan Yuli, sakamakon arangama, da kisa a fili, da kuma harin bama-bamai da sojojin mamayar Isra’ila suka kai ya kai 2,047.
Hukumar da ke sa ido kan lamarin ta yi bayanin cewa, “a ci gaba da bincike, akwai yiyuwar adadin wadanda suka mutu ya karu, ganin cewa akwai wadanda suka bace daga irin wadannan abubuwan da har yanzu ba a tantance makomarsu ba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Tawagar Yan Wasan Damben Gargajiya Ta Iran Ta Zama Zakara A Damben Ta Duniya September 16, 2025 An Fara Taron Hukumar Makamashin Nukliya Ta Duniya IAEA Karo Na 69 A Birnin Vienna September 16, 2025 Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza September 16, 2025 Makaman ‘Drons’ Na Yemen Sun Fada Kan Wurare Masu Muhimmanci A HKI September 16, 2025 Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila September 16, 2025 Ministan Tsaron Venezuela Ya Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Juyin Mulki A Kasar September 16, 2025 Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya September 16, 2025 Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai September 15, 2025 Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci