Aminiya:
2025-09-18@01:00:37 GMT

Miji ya yi yunƙurin kashe matarsa kan zargin maita

Published: 4th, March 2025 GMT

Kotu ta tsare wani magidanci a gidan yari kan zargin barazana ga rayuwar matarsa da yake zargin ta da maita.

Babbar Kotun Musulunci da ke Gazawa a Jihar Kano ta tsare mutumin ne bayan ya yi barazana tare da yunƙurin kai wa matar tasa farmaki da adda.

Mai gabatar da ƙara, Sadiq Yusuf ya shaida wa kotun cewa mutumin ya yi yunƙurin aika-aikan ne bisa zargin matarsa da kama kuruwar ɗansu da ya jima yana fama da rashin lafiya.

Magidancin da ke zaune a ƙauyen Gawo da iyalin nasa ya musanta tuhumar da ake masa, don haka, Alƙali Nura Ahmad ya ba da umarnin tsare shi a gidan yari.

Bidiyon batsa: Kotu ta ɗaure ’yan Tiktok a gidan yari a Kano NAJERIYA A YAU: Abin Da Ya Sa Ba Mu Bayar da ‘Ramadan Basket’ Ba

Ya kuma ɗage shari’ar zuwa ranar 20 ga watan nan na Maris domin masu ƙara su gabatar da shaidu.

Ɓari: Matan aure sun yi wa wata barazana

A wata sabuwa kuma, an gurfanar da wasu matan aure biyu kan zargin yin barazana ga wata da suke zargi da haddasa zubewar juna biyun dayarsu.

Kotun da ke zamanta a unguwar Danbare, Ƙaramar Hukumar Kumbotso, na zargin matan auren da haɗa baki da yunƙurin aikata laifi.

Ana zargin matan waɗanda mazauna unguwar Rimin Auzinawa da ke Ƙaramar Hukumar Ungogo da barazanar ga matar tare da zargin ta da haddasa zubewar juna biyun dayarsu.

Sai dai sun musanta zargin, inda daga baya alƙalin, Khadi Munzali Idris Gwadabe, ya ba da belinsu, bayan lura da yanayin lafiyar wadda ta yi ɓarin, da ke murmurewa.

Ya kuma daga sauraron shari’ar zuwa ranar 16 watan Afrilu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: matar zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Nijeriya dai ta daɗe tana fama da ta’addancin Boko Haram da ISWAP a Arewa Maso Gabas.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara