Majalisar Dattawa ta sanar da cewa a halin yanzu ba ta da hurumin gudanar da bincike kan zargin cin zarafi da Sanata Natasha Akpoti-Uduagha ke yi wa Sanata Godswill Akpabio.

A bayan nan dai ana ci gaba da samun ƙarin kiraye-kirayen gudanar da cikakken bincike kan zargin da Sanata Natasha ta yi wa Shugaban Majalisar Dattawan, Godswill Akpabio a kan cewar ta ƙi ba shi haɗin kai, shi ne ya sa ya ke yi mata bita da ƙulli.

NDLEA ta cafke madugun fataucin miyagun ƙwayoyi bayan shekaru 17 yana ɓuya An sake zaɓen Obasa Kakakin Majalisar Legas

Sanata Natasha Akpoti Uduaghan daga Jihar Kogi ta yi wannan zargin ne jim kaɗan bayan da aka soma kai ruwa rana tsakaninta da Sanata Akpabio, lamarin da ya sa a yanzu Majalisar Dattawan ke binciken Sanata Natasha bisa zargin nuna rashin ɗa’a.

Ita dai Sanata Natasha ta nuna tirjiya bayan da aka sauya mata wurin zama a zauren Majalisar Dattawa inda ta yi zargin cewa matakin na da nufin rufe mata baki tare da kawo mata cikas wajen gudanar da aikinta.

Saboda irin ƙurar da ta tayar sai Majalisar ta yanke shawarar cewa Sanatar ta bayyana a gaban kwamitin ladabtarwa domin ta kare kanta.

Sai dai kafin ta bayyana a gaban kwamitin, Sanata Natasha a wata hira da gidan talibijin na Arise, ta yi zargin cewa shugaban majalisar Akpabio ya nemi ya yi lalata da ita kuma ba ta ba shi haɗin kai ba, shi ne abin da ya janyo ya sa mata ƙahon zuƙa har aka sauya mata wurin zama.

Sanata Natasha ta kuma maka shugaban Majalisar Dattawan a gaban kuliya inda take neman diyyar Naira biliyan 100 saboda zargin ɓata mata suna.

Dalilin da ba za mu binciki Akpabio ba — Majalisar Dattawa

Sai a wata hira da gidan Talabijin na Arise a ranar Litinin, Shugaban Kwamitin Hulɗa da Jama’a na Majalisar Dattawan, Sanata Yemi Adaramodu, ya ce ba za su iya bincikar Sanata Akpabio saboda har kawo yanzu Sanata Natasha da ke zarginsa da cin zarafi ba ta shigar da wani ƙorafi a hukumance ba.

Sanata Adaramodu na jam’iyyar APC daga Jihar Ekiti ya ce babu wani ƙorafi da Sanata Natasha ta shigar a gaban kwamitin ɗa’a da ladabtarwa ko kwamitin karɓar ƙorafi ballantana a gudanar da bincike a kan lamarin.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: cin zarafi Majalisar Dattawa Majalisar Dattawan Majalisar Dattawa gaban kwamitin

এছাড়াও পড়ুন:

An Horas Da Mata 600 Kan Abincin Yara Mai Gina Jiki A Jigawa

A wani yunkuri na yaki da rashin abinci mai gina jiki da kuma karfafa tattalin arzikin mata a jihar Jigawa, Gwamna Umar Namadi ya jagoranci bikin yaye mata 600 da suka samu horo kan yadda ake sarrafa abincin yara mai gina jiki daga kayayyakin da ake samarwa a gida, wanda aka fi sani da “Tom Brown”.

Malam Umar Namadi ya bayyana wannan shiri a matsayin wata dabara ta cikin gida da aka kirkira domin shawo kan matsalolin rashin abinci mai gina jiki a tsakanin yara, da kuma karfafa tattalin arzikin mata.

“Muna matukar godewa Allah da ya ba mu hikima da basira don kirkirar wannan tsari wanda zai taimaka mana mu cimma manufofi da dama a lokaci guda.” In ji shi.

“Bayan bai wa wadanda aka horar damar samun ingantacciyar hanyar dogaro da kai, wannan kuma wata babbar dabara ce wajen yaki da rashin abinci mai gina jiki a cikin yara. Hakan kuma zai taimaka wajen hana matsalolin nakasa a kwakwalwa, domin kare damar girman yaron yadda ya dace.”

Gwamnan ya jaddada cewa Tom Brown, wanda wasu ke kira da Kwashpap, an tabbatar da ingancinsa wajen magance matsalar rashin matsakaicin abinci mai gina jiki (Moderate Acute Malnutrition – MAM) ta hanyar hadin kayan gida kamar gero, gyada da wake.

Ya kara da cewa wannan shiri na da cikakken daidaito da manufofin gwamnatin jihar na bunkasa abinci mai gina jiki, wanda ya fara haifar da sakamako mai kyau.

A cewarsa, kowace daga cikin matan 600 da suka amfana da shirin ta samu kayan fara sana’a da suka hada da injin rufe roba da kayan masarufi domin farawa da sarrafa Tom Brown a matakin gida.

Namadi ya bayyana cewa kananan hukumomi da cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko a fadin jihar za su hada gwiwa domin tabbatar da amfani da kuma shigar da wadannan kayayyaki cikin shirye-shiryen inganta abincin yara.

Ya ce, horar da wadannan mata 600 wani bangare ne na kokarin gwamnati wajen hanzarta samun ci gaba a fannin kula da rayuwar al’ummar,  da ingantacciyar lafiyar yara.

Gwamna Namadi ya kuma sake jaddada kudirin gwamnatinsa na rage dogaro da kayan abinci masu tsada da ake shigowa da su daga kasashen waje, ta hanyar bunkasa hanyoyin cikin gida masu saukin samu da kuma arha.

Ya sanar da cewa jihar Jigawa na cikin jerin jihohin da ke amfana da shirin ANRiN na Bankin Duniya, wanda ke mayar da hankali kan kara samun damar kula da lafiyayyen abinci ga mata da yara ‘yan kasa da shekaru biyar.

“Babban burin wannan shiri shi ne kara yawan amfani da ingantattun hanyoyin kula da abinci ga mata masu juna biyu da masu shayarwa da kuma yara ‘yan kasa da shekaru biyar. Wannan yana da nasaba da hangenmu cewa shirin ANRiN zai taka rawar gani wajen hanzarta ci gabanmu ta bangaren samar da abinci mai gina jiki ga yara.”

 

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
  • An Horas Da Mata 600 Kan Abincin Yara Mai Gina Jiki A Jigawa
  • INEC Ta Gudanar da Taron Masu Ruwa da Tsaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi na Babura/Garki
  • Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana
  • Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana
  • Majalisa ta ba NNPCL mako uku ya yi mata bayanin inda tirilyan 210 ta shiga
  • Kwamitin Neman Sabuwar Karamar Hukumar Kanya Babba Ya Gabatar Da Takardar Bukatarsa Ga Majalisar Dattawa
  • Kwamitin Aikin Hajjin 2025 Na Jihar Kano Ya Kammala Rahoton Aikinsa Na Wucin Gadi