Dalilin da ba za mu binciki Akpabio kan zargin cin zarafin Natasha ba — Majalisar Dattawa
Published: 4th, March 2025 GMT
Majalisar Dattawa ta sanar da cewa a halin yanzu ba ta da hurumin gudanar da bincike kan zargin cin zarafi da Sanata Natasha Akpoti-Uduagha ke yi wa Sanata Godswill Akpabio.
A bayan nan dai ana ci gaba da samun ƙarin kiraye-kirayen gudanar da cikakken bincike kan zargin da Sanata Natasha ta yi wa Shugaban Majalisar Dattawan, Godswill Akpabio a kan cewar ta ƙi ba shi haɗin kai, shi ne ya sa ya ke yi mata bita da ƙulli.
Sanata Natasha Akpoti Uduaghan daga Jihar Kogi ta yi wannan zargin ne jim kaɗan bayan da aka soma kai ruwa rana tsakaninta da Sanata Akpabio, lamarin da ya sa a yanzu Majalisar Dattawan ke binciken Sanata Natasha bisa zargin nuna rashin ɗa’a.
Ita dai Sanata Natasha ta nuna tirjiya bayan da aka sauya mata wurin zama a zauren Majalisar Dattawa inda ta yi zargin cewa matakin na da nufin rufe mata baki tare da kawo mata cikas wajen gudanar da aikinta.
Saboda irin ƙurar da ta tayar sai Majalisar ta yanke shawarar cewa Sanatar ta bayyana a gaban kwamitin ladabtarwa domin ta kare kanta.
Sai dai kafin ta bayyana a gaban kwamitin, Sanata Natasha a wata hira da gidan talibijin na Arise, ta yi zargin cewa shugaban majalisar Akpabio ya nemi ya yi lalata da ita kuma ba ta ba shi haɗin kai ba, shi ne abin da ya janyo ya sa mata ƙahon zuƙa har aka sauya mata wurin zama.
Sanata Natasha ta kuma maka shugaban Majalisar Dattawan a gaban kuliya inda take neman diyyar Naira biliyan 100 saboda zargin ɓata mata suna.
Dalilin da ba za mu binciki Akpabio ba — Majalisar DattawaSai a wata hira da gidan Talabijin na Arise a ranar Litinin, Shugaban Kwamitin Hulɗa da Jama’a na Majalisar Dattawan, Sanata Yemi Adaramodu, ya ce ba za su iya bincikar Sanata Akpabio saboda har kawo yanzu Sanata Natasha da ke zarginsa da cin zarafi ba ta shigar da wani ƙorafi a hukumance ba.
Sanata Adaramodu na jam’iyyar APC daga Jihar Ekiti ya ce babu wani ƙorafi da Sanata Natasha ta shigar a gaban kwamitin ɗa’a da ladabtarwa ko kwamitin karɓar ƙorafi ballantana a gudanar da bincike a kan lamarin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: cin zarafi Majalisar Dattawa Majalisar Dattawan Majalisar Dattawa gaban kwamitin
এছাড়াও পড়ুন:
Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta ce mayar da martani ga gwamnatin Isra’ila hakki ne na shari’a ga Iran kamar yadda doka ta 51 ta kundin tsarin mulkin MDD ta tanada.
Da farko dai ma’aikatar ta mika ta’aziyyar shahadar wasu kwamandoji da jami’an kasar Iran a harin da Isra’ila ta kai wa kasar.
“Hare-haren da gwamnatin sahyoniyawan ta kai wa Iran sun sabawa doka ta 4 sakin layi na 2 na kundin tsarin mulkin majalisar dinkin duniya a matsayin wani mataki na wuce gona da iri kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran, kuma Iran tana da hakki na shari’a na halal ta mayar da martani kan wannan zalunci kamar yadda yake a cikin sashe na 51 na kundin tsarin mulkin majalisar dinkin duniya.
Sojojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen kare al’ummar Iran da dukkan karfinsu.”
“Jamhuriyar Musulunci ta Iran a matsayinta na mamba a Majalisar Dinkin Duniya, tana mai jaddada wajibcin kwamitin sulhu na majalisar dinkin duniya na daukar matakin da ya dace wajen tunkarar matsalar zaman lafiya da tsaro na kasa da kasa, sakamakon wuce gona da iri da gwamnatin sahyoniyawan take yi wa Iran.
“Dukkan kasashe mambobin Majalisar Dinkin Duniya, musamman na shiyya da na Musulunci, da ‘yan gwagwarmaya, da dukkan duniya ana sa ran nan take za su yi Allah-wadai da wannan aika-aika da kuma daukar matakin gaggawa da hadin gwiwa don tinkarar wannan kasada mai hatsarin gaske wadda ko shakka babu ta nuna yadda zaman lafiya da tsaro a duniya ke cikin wata babbar barazana da ba a taba ganin irinsa ba.”
Iran, ta kuma babu shakka wannan danyen aikin da Isra’ila ta aikata ya samu sahalewar Amurka, don haka a cewar Tehran, Amurka na da hannu a wannan hare haren na Isra’ila.